25.8.07

KWADON DABI'AR DAN ADAM DA MABUDINTA

ABUL HASAN ANNADAWY


Auwal Muhammad Abdulkadir
aazarema@yahoo.com
25-8-07m / 11-8-1228
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata masa ba irin sauran masu gyaran da ke zuwa gidaje ta baya ko su sadado ta taga bane , masu yaki da wasu cututtukan zamantakewa da aibubbukan halaye kawai ba , sai ka samu daga cikinsu akwai masu sa’ar gusar da wasu a sassan wasu garuruwa na dan wani lokaci, wani ma ya mutu bai cimma burinsa ba.
To amma shi manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata yazo wa gidan gyara ta kofarsa , kuma ya sanya wa kwadon dabi’ar dan’adam mabudinta , wannan kwadon yana dawuyar sha’ani saboda bude shi ya gagari masu sauyi kafun manzanci dama duk wanda yai kokarin bude shi bayan shi ba tare da mabudinsa ba.
Ya kira jama’a zuwa ga imani da Allah shi kadai, da kin gumaka da bauta da kafircewa dagutu, don haka ya mike cikin jama’a yana cewa “ ya ku mutane ! Kuce ba abun bautawa da gaskiya sai Allah ku rabauta ( ku sami rabo) ‘’ ya kuma kira su zuwa ga imani da manzanci
da imani da lahira .
Mahatma ghandi na kasar hindu a rayuwarsa ta siyasa da gwagwarma ya takaita jagorancinsa da gwagwarmayar sa kan ka’idoji biyu ne .
Na farko: wanda shine takensa (ba muzgunawa ba kare kai) yayi kira zuwa ga wannan ka’ida a matsayin addini da falsafa cikin hudubobinsa da makalunsa da kuma jaridunsa. Ya karar da karfinsa kan haka , to da yake hanyar daya dauka ba hanya ce mai zurfi wajen sauyin zuciya ba bata yi wani tasirin azo agani wa mutanen hindu ba , don haka suka hure ta , suka kashe rabin miliyan na musulmi a East Punjab da Delhi a 1947 miladiya, daga karshe shi ghandin aka masa kisan gilla dukda daukaka shi da bauta masa da wasu suke yi.
Na biyu: shine shafe matsalar fifiko tsakanin kabila da kabila , wanda baiyi nasarar kirki ba, wannan yankakken dalili ne cewa manhajin annabawa shine ya mafi kyau wajen gyara da sauyi.
fassara daga littafin (( Rashin da duniya tayi samakon faduwar musulmai)) na malam Hasan Annadawi.

18.8.07

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRACI

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRAICI
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR

6/8/1428h-19/8/07m

BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM
Sanannen abune cewa kasashe masu kaffa-kaffa da
addinin su da al'adunsu na kwarai suna kokarin maida
finafinai da wasan kwaikwayo wata kafa ta tattauna matsalar
alumma da tarbiya da bada tunani na gari, sabanin halinda
muke a kasar hausa na karkatar da wannan dama zuwa
gwada kwarewa wajen nuna rashin kunya da da koyawa
manyan gobe munanan dabi'u daga baya kuma sai ace ana
kokarin gyara tarbiya to lallai bamu ba tarbiya har duniya ta
tashi indai yan daba da mata masu cin gashin kansu da
wadanda aka kasa tarbiyarsu suka gudu suka bar tarbiya su
-ne masu tarbiya kai abun dariya da takaici duk da haka
shuwagabanni da wadanda abun ya shafa basu yi yunkurin
hanawa ko kokarin garkatar da akalar fina-finan izuwa koyar
da tarbiyar gaskiya ba . to yanzu abun yakai ga dole kowa ya
ciza yatsa , akwai matukar da takaici ace yar fim ta fito tsirara
har na tsawon dakikai takwas kan gado sannan wani yazo ya
haukanta yayi tsiyar da zaiyi da ita, sannan yayi wani irin
nau'i na wasa da maniyinsa kan cinyarta , kai ! wallahi ,
na'uzu billahi minashshaidanirrajim! wani irin dabbanci kenan?
kuma abun mamaki harda cewa '' a gafarcemu'' amma
wannan yarinya taci sunanta ''HIYANA'' don kuwa ta ha'inci
duk musulmin duniya, ta kuma tona asirin musulmin najeriya.
Duk wani mai zurfin tunani yasan hakan zata faru tunda
kokari suke su kwaikwayi [nigerian film] su kuwa wannan ba
bako bane gunsu, ga wani abunda na taba karantawa jaridar
gaskiya tafi kwabo ''GTK: To, a matsayinki na wadda take fitowa a fina-finan
Hausa da na Turanci, yaya za ki kwatanta bambancin da ke
tsakanin fina-finanmu na Arewa da kuma na Kudanci?
HAUWA MAINA: Ai dai wannan ne ko kuma aka tambaya, za
ku iya fadin bambancin (dariya).
GTK: Amma da yake ke kina cikin harkar ne, ina ganin ke ya
fi cancanta ki yi mana bayani.

HAUWA MAINA: To shi kenan, a gaskiya, ’yan Kudu sun yi
mana fintinkau in dai za a yi maganar gaskiya ce. Amma
Alhamdulillahi mu ma mun fara shiga sahunsu, saboda idan
aka yi la’akari da irin na’urorin da suke amfani da su, to,
yanzu mu ma mun fara samun irin wa]dannan na’urorin. Haka
kuma ’yan wasanmu na Hausa su ma yanzu sun zaburo, suna
kuma kokari sosai. Saboda haka nan ba da jimawa ba za mu
rika hada kafada da kafada da su.''

Hakika abun daya ban mamaki cikin wannan al'amari babu
kamar wasu masu kokarin wanketa da cewa ai ba fim din
tsiraici bane, saboda wannan wani abu ne tsakaninta da
saurayinta bai da alaka da fim, to amma ai ita jaruma ce a
wannan harka ta tarbiya, wa ya sani ko ta sadaukar da kanta
ne wajen gyara al'adun banza har ta fara yada tarbiya kyauta
ana yada ta a blue tooth cikin kayan mutunci , domin ayi koyi
da ita, sannan an sakar muku haka ne , shin wannan baya
gwada cewa wata ran za'a yi hakan a tsare da furodusa da
dukkan shikashikai da sharuddan fim.

sannan wasu kuma sun bige da cewa taci mutuncin hausa-
fulani ina ruwan wannan matsala da hausa fulani , wasu na
cewa daman ba hausawa bane masu yi , hakika wannan
karya ce mai girma da neman wanke kai na banza da wofi ,
to kai in ma haka ne , waya basu izinin shigowa kano, jama'a
kar mu rudi kammu, hausa fulani dai a duniya zamu bar shi
ba wani abu mai anfani gun Allah sai musulunci.

IYAYE : sune kashin bayan tarbiyar 'ya'ya kuma sune
matakin da idan yaro ya rasa ko sukai sakaci dashi rayuwarsa
zata shiga wani yanayi wanda bara aji dadin karshenta ba,
wani yana cewa '' uwa makaranta ce idan ka shirya ta kamar
ka shirya al'umma ne'' kuma kamar yadda kowa ya sani
wadannan masu cin abinci da lalata tarbiyar manyan gobe
galibinsu in bamu ce duka ba sun fuskanci matsala da iyaye
kamar auren dole ko rashin mai riko mai kyau ko rashin tsawa
da kwaba don haka dole iyaye su dau hakurin daukan kaso
mai girma na laifi saboda kaso mai girman ba suke dashi
wajen jibintan yayansu da kuma damar tarbiya.

YAN WASA: saboda sune masu fuskantar da wannan
matsala zuwa ga alumma kai tsaye don haka duk da barrantar
da kan- su da wasu uzurori da suke bayarwa wanda zai yi
wuya su kansu su yarda da su a cikin zukatansu balle
al'umma gaba daya. Su dai kokarin su dole sai sun kwaikwayi turawa alhali kuwa
kowa yana kokarin bada gudumawane daidai al'ummarsa,
idan bature da baturiya sukai wani rashin kunya a wasan
kwaikwayo to saiku duba cewa to shin kowa a cikin jama'arku
ba rike ya ke da addini ba ? ba tare yake da mafadi ba? Shin
burgewa a garemu shine mu fita daga shingen iyaye da
sunan yanci? Wadannan banbance-banbance na addini da
al'ada idan ba'a duba su ba to zamu jima cikin wannan rami,
mu fito mun yi kura duk wanda ya kallemu ba zai iya
maimaitawa ba.

SHUGABANNI: wato duk Wanda yake da damar fada aji
amma bai hango matsalar da zata iya jawowa masu
zuwa ba, ko ya hango baiyi kokarin kawo sauyi ba .

Daga karshe ina kara rokon wanda abun ya shafa da suyi
hattara wajen daidaita wannan wasa inda zaiyi daidai da
addinin jama'arsu da al'adunsu na kwarai , inba haka ba muyi batan bakatantan bamu ga namu bamu ga nasu .

Allah ya raba mu da sharrin shaidan.

11.8.07

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR
aazarema@yahoo.com
Da yawa mun rudu da sanimmu ko bada sanimmu ba kan abunda amurka da yammacin duniya ke farfaganda kai, na yanci, hakkin bil'adama ,sakulanci (secularism), yakan wariya , girmama addinindan adam ko da ya yake, da sauransu . muna kuma ganin cewa wannan wani cigaba ne sakamakon kokarinsu na amfanar da halittu wanda ba'a sansu ba a baya , wanda kuwa duk wadannan addinin musulunci ya baiyana na kwaransu sannan yayi kafar angulu da wofi daga ciki da isassun dalilai na nassi (kurani da hadisi) ko na hankali .
Alkurani ya tabbatar mana cewa manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] rahama ne ga dukkanin halittu , sannan musulunci shine ya sauya alummar larabawa da ke cikin mummunan yanayi na zamantakewa da siyasa da dukkan sassan rayuwa, ibnu abbas yana cewa: “idan kana so kaga yanda jahilcin larabawa ya kai sai ka karanta fadin Allah madaukakin sarki: “ Lalle ne wadanda suka kashe diyansu , saboda wauta bada ilimi ba sunyi hasara ! kuma suka haramta abinda Allah ya azurtasu bisa kirkira karya ga Allah lalle ne sun bace basu kasance shiryaiyu ba ” .[6:140].
Bayani kan sauyin da musulunci ya kawo ba boyaiye bane saidai abunda ya shige mana duhu musulmanmu da kafiranmu shine shin musulunci yazo da abubuwanda yammaci ke takama dasu koko? Kamar yadda muka yi bayani a baya ya tabbatar da wasu, ya kuma sa wasu a gefe.
Zamu iya ganin yadda musulunci ya kimata dan adam cikin fadin Allah madaukakin sarki: “ kuma lalle mun girmama 'yan adam , kuma muka dauke su a cikin kasa da teku , kuma muka azurtasu daga abubuwa masu dadi , kuma muka fifitasu a kan da yawa daga wadanda muka halitta, fifitawa ” [ 17 :70] .
Manzon Allah [tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] da aka tambayeshi hakkin mace gun mijinta sai yace “ ka ciyar da ita idan kaci , kuma ka tufatar da ita idan ka tufata , kuma kar ka bugeta a fuska , kada kuma ci mutuncinta , kar kuma ka kaurace mata saidai a cikin gida” wannan hadisi an samo shi ne kafin wani abu da ake cewa (CEDAW) . Musulunci har wayau ya tabbatar da kulawa da tausayawa yara kamar yadda yazo cikin hadisi cewa wani bakauye yaga manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] ya sunbanci yaro sai yayi mamaki yace shi yana da yara goma amma bai taba sunbantar ko daya ba , sai abun yayi nauyi wa manzon Allah tsira da aminci sutabbata a gareshi har yace: “ to ya zanyi idan Allah ya zare rahama a zuciyarku¡?”.
Musulunci bai ba wariya kafar shiga ba Allah yana cewa “yaku mutane lalle ne mun halittaku daga na miji da mace , kuma muka sanyaku dangogi da kabiloli domin kusan juna”.[49:13]. Kuma cikin hadisi Abu zarri Allah ya yarda shi ya bada labari cewa ya samu sabani da wani danuwansa wanda mahaifiyarsa ba'ajamiya ce ( ba balarabiya ba) sai ya aibace shi da mahaifiyarsa , da labari ya isa wa annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi sai yace: ya kai abu zarri, lallai akwai jahiliya a tare da kai, su 'yan'uwanku ne Allah ya sanya su a cikin hannun ku , don haka ku ciyar dasu daga abunda kuke ci ,kuma ku tufatar dasu daga abunda kuke tufata dashi , kuma kar ku daura musu nauyin da baza su iyaba, idan kuma kun daura musu to ku taimake su,” kamar yadda Allah ya nuna cewa tsoronsa kawai shine fifiko tsakanin jama'a kan wasu sabanin yahudawa masu riya cewa sune zababbun agun Allah [ God’s favoured nation] , kuma sune masu gudanar da tsarin mulkinsu kan tatsuniyoyin da suke samowa daga Attaurar da hannu yayi wasa ciki , kenan su basa raba addini da siyasa amma duk da haka tana samun kariya daga amurka da sauran manyan kasashe , kai har shi kansa BUSH ya kasa aiki da tsarin “ na sarki na fada , na Allah na masallaci” ko “[ Give unto God’s , what a God’s, and unto Caesar what a Caesar;s] tun da an tambayeshi wanene babban malamin falsafa a siyasar sa sai ya kada baki yace : yesu almasihu”. Girmama addinnai kuwa ma'anarsa a musulunci ba shine jin cewa wani addini koma bayan musulunci shine gaskiya ba , innama ma'anarsa zama da kafirai ba tare da tsangwama ba idan an yi alkawarin lumana dasu , Annabi kuwa yayi zaman alkawarida da yahudawa a madina dukda cewa daidaikunsu suna kokarin kashe shi kamar yadda wata bayahudiya ta sa masa guba cikin abinci , kuma sunyi kokarin jefo masa dutsen markade daga kan bene , amma duk da haka bai far musu ba saida suka saba alkawari a fili da suka hada kai da mutanen makkah wajen yakarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. Wannan shine yasha banban da abunda masu kirayen-kirayen sukeyi na tuhuma addini daya cikin dubban addinan duniya da taaddanci , ko jifa da littafin addini daya cikin kazanta , ko siffanta manzon wani addini daya da harijanci da ta'addanci, duk wannan suna yine domin kara kwanakin daularsu , amma kuwa akasin haka ne ke faruwa don kuwa duk sanda suka kunna wata wuta kan musulunci sai samarukansu sun bi diddigi sun fahimci karyansu kuma sakamakon haka su shiga musulunci jama'a- jama'a , Allah ta'alah yana cewa :[ lalle ne wadanda suka kafirta suna ciyarda dukiyoyinsu, domin su tare hanyar Allah , to zasu ciyar da ita ,sa'annan ta kasance nadama a kansu , sa’annan kuma a rinjayesu”, [8:36], kuma yana cewa “ lalle ne , wadanda suka zo da karya wadansu jama'a ne daga cikinku , kada kuyi tsammanin hakan sharri ne a gare ku, a'a alheri ne a gare ku”. [24:11].

Reality

There are many wide spread ideas among westernersprophet Muhammad peace be upon to him , Qoran and islam in general.
Accoding to conservertives ''prophet Muhammad's life is bloody , his teaching is vicious ,and he is founder of the world most intolerancAe religion (islam).
such kind of un objective accusation awake there peaple for searching truth and reality about prophet Muhammad not from his enemy but from what has been sent down to him , and his wisdom .