26.10.07

BIBIYAR LITTAFIN ‘’SUDA’’

15/shauwal/ -h _26/11/2007

Malam Kabiru Yakasai ba shakka haziki ne mai matukar hikima , da alama kuwa hannunsa ya jima yana goga alkalami kan takarda .
Duk wannan takaitaccen yabon ba wai nasan shi bane , saidai na kwatanta zakakurancinsa ne sakamakon karanta littafinsa mai suna ‘’suda’’ littafinda ya hada nishadantarwa da tarbiya da azanci .

Shekaran jiya nake karanta shi lokacinda na bakonci dangina a omdurman na jamhuriyar sudan , amma lokaci zuwa lokaci sai in kyalkyale da dariya saboda in nayi hakuri a taran aradu da kan dankani wani lokaci to wani lokacin kuma bazan iya hana bakina ‘yancin dariya ba.

Mun kasance muna kishirwan mawallafa irin malam Kabiru ruwan wankin daudar zamantakewa , don kuwa mun kosa da masu kwashe baiwar talifi da Allah ta’ala ya musu sui ta yawo tsakanin so da ki , da soyaiya da kiyaiya kamar mu hausawa wata al’umma ce wacca bata da wata matsala sai soyaiya .

Malam ya fara bada labarin baba suda a takaice wanda shi kuma shine ya ba yara labarin rigingimun dankane, kuma ni a fahimta ta malam ya nusar damu ne cewa tara yara da basu labaru wata hanyace ta tarbiya , kamar yadda Allah ta'ala ya dauki wannan salo a kaso mai girma na Alkur’ni kamar : suratu Yusufa kacokam dinta ta bada labarin annanbi yusufa ne , ta kuma bada mahimmanci kan al’amuran zamantakewa ,wasu surori kuma annabi Isa , Musa , Dauda da Sulaiman , Ibrahin da sauransu , da labarin sarakuna kamar Fir’auna da Lamarudu , duk wannan domin mu dau izna .

Wani abu mai tabbatar mana cewa mawallafin ya na da hadafin azo agani wajen talifin wannan littafin shine inda yayi bayanin cewa baba suda ya bawa yara wannan labarin ne saboda ya umurci wani yaro da ya sai wa alkaki da ya samma dan’uwansa da ya makara bai samu ba , sai yaron yaki daga nan sai ya kwabe su da su bar rowa daga nan ya fara basu labarun wahalhalun da dankane ya sha wanda galibinsu sakamakon rowarsa da son kudinsa ne kamar dan canjin yahudawa.
Mawallafin yayi bulala wa sharifan karya dama na gaske masu ci da salsalar nasaba , yan danfara , barayin zaune , sannan yayi bayanin yadda dankane ya tashi daga almajiri zuwa matsayin alkali zuwa waziri har sanda yayi juyin mulki ya dawo sarki mai cikkakken iko daga nan kuma yayi karkon kifi ya koma tunku , abun mamaki!! .

Sannan yaci gaba da tsumage ‘yandaudu da malaman tsubbu 'yan kawo rago kawo zakara mai kwai, da masu ruwan ido , har lokacinda dankane ya ga ba harkar da bai shiga ba amma bai ci nasara ba saura masa harka daya da bai jarraba ba itace harkar kamun kai da bin addini sauda kafa , daga nan ya yasar da duk wani shashanci har ma ya koma alaramma mai jan baki a ramalana.

Saidai malam kabiru abunda ya daure mun kai wai shin akwai wani nassi daga kur’ani ko hadisi mai tabbatar da cewa sharu wuta bata kama shi koko dai siddabaru da rufa ido sharifan suke yi ? .
Har wayau aganina ba kai tsaye ba ka daurewa bokaye da malaman tsubbu gindi in da kayi bayanin wani malami mai gudun duniya ya ba dankane wuridin kiran aljanu to amma wannan malamin ba kamar yanda kayi bayani cewa malamin Allah da annabi bane tunda wannan shirka ne hada Allah da wani ne , Allah kuwa yana cewa ‘’ idan bayina suka tambayeka dangane da ni to ni a kusa nake ina amsa kiran mai kira in ya kirani ’’

Wani abun da na lura dashi kan littafin ‘‘ suda‘‘ shine jama’a sunfi saninsa da ‘‘Dankane‘‘ , sai naga dama malam kabiru ya rada wa littafin Suna DANKANE , sannan kalmar dankane wani sa’in malam yakan sa mata wasalin [e] wani lokaci kuma wasalin {I} tsammanina so yake ya nusar da mu cewa duka hausa ce karbabbiya dankani da dankane.
Zanso ku karanta littafin SUDA sai dai kar ku zargi malam kabiru idan bakin ku ya barke don dariya.
Wassalam.

5.10.07

BIBIYAR YAKIN DUNIYA NA BIYU


A LOKACINDA JAMUS TA YAKI POLAND ,A WATAN SATUMBA 1939 ,SHEKARA ASHIRIN BAYAN YAKI DUNIYA NA DAYA , HAR ANYI TSAMMANIN ZAMAN LAFIYA YA DAWWAMA, SAI GASHI, ANGULU TA KOMA GIDANTA NA TSAMIYA, SABODA JAMUS DA JAPAN SUNYI KOKARIN BAZA MULKINSU HAR KASASHEN TURAI DA AFRICA

DA GABAS TA TSAKIYA SAIDAI SOJOJIN HADIN GWIWA SUN FAR MUSU BAYAN SUN BIYA WASU BUKATUNSU BANDA WASU ,MASU KIDAYA SUNA CEWA RAYIN MUTUM DUBU HAMSINNE YA FITA TA INDA WASU SUKACE BA A SAN YAWANSUBA.
DA GA CIKIN WAKI OIN DA ZAN IYA TUINAWA SHINE YAKINDAI YUAFARANE WATAN SATUMBA 1939 ,WATAN AFRILU HITILA ,YAYI KAFAR ANGULU GA YARJEJENIYAR SHEKARAR 1939 TSAKANINSA DA BARITANIYA, SANNANN WATAN AGUSTA NAZI TA KULLA YARJEJENIYA ZAMAN LAFIYA DA SABIYAWA SHE KUWA HITILA YAYI HAKANE DOMIN KADA RASHA TACE UFFAN,YAYIN DA ZE KAIWA POLLAN HARI,WATO HARIN DAYA KAI MATA A SATUMBA SANNAN DAGA CIKIN TUN AWA A WATAN AFRILU 1940
JAMUS TA AUKAWA DENMARK, TA INDA DA KEWAYE IYA KOKINTA ITA KUMA DENMARK TA MIKA WUYA .
A KUMA WATAN MAYU JAMUS TA KEWAYE BELGIKA A GEFE GUDA KUMA FARANSA DA BARITANIYA SUNYI KOKARIN SHIGOWA BELGIKA SAI JAMUS TA FARMUSU ,,SANNAN JAMUS TA KAMA AREWACIN FARANSA CIKIN SAUKI ABINDA YABASU MAMAKI, HAR SUKA DAKATA DA DOMAIN KARA SHIRI FARANSA DA RUNDUNARTA NAN TAKE TAFRAS MUSU/
SANNAN A WATAN YULI, JAMUS TA KEWAYE FARISA ,KUMA TA KEWAYE TSUBURIN CHANEL, A WATA MAI ZUWA KUMA HITILA YA UMARCI RUNDUNARSA DA AUKAWA BARITANIYA
WATA BABBAR WAKIM A KUMA ITACE HARE HAREN SAMA MASU GIRMA WANDA JAMUS TA ZAZZAGE A BIRNIN LONDON,ITAMA LONDON DA DAU FANSA WANDA BAIKAI NA JAMUS BA.
CIKIN SHEKARAR 1941 WATAN YULI,KWATSAM SAI YARJEJENIYAR TSAGAITA KAWO HARI,TA KARE TSAKANIN JAMUS DA SABIYAWA,YAYINDA JAMUS TAKAI MUMMNAN HARINDA TARIHI YA BUGA MASA HATIMI.
SANNAN CIKIN SHEKARAR 1942 WATAN NUWAMBA JAMUS TA MAMAYE KUDANCIN FARANSA DOMIN SU KAMA JIRAGEN RUWANSU SAI DAI FARANSA TA KONA DOMIN KADA YA KOMA ABOKAN GABA.
SANNAN CIKIN SHEKARAR 1934 WATAN AFRILU BARITANIYA TA YAUDARI JAMUS YAU DARAR DA TA BADA MAMAKI TA YANDA SUKA SANYA TAKARDA MAI NUNA CEWA ZASU YAKI WURARE GUDA BIYU A GIRKA, SANNAN SUKA YASAR A GEFAN TEKUN ANDALUS TAYANDA JAMUS ZASU TSUNTA AMMA SU SUNA SONE SUKAI HARI SICILY DOMIN KADA JAMUS SU FAR MUSU DON HAKA JAMUS TAKAI RUNDUNARTA GIRKAS SU KUMA SUN YAKI SICILY .
S HEKARA 1944 WATAN YULI HITILA YAYI ZAMA DA JIGA JIGAN HUKUMARSA DAN GANEDA YAKIN DA SUKEYI KO DAYA SUNKUYA DOMIN YA DUBA TASWIRA SAI WANI BOMB YA FASHE WANDA MUTUN HUDU SUKA RASU SHE KUMA TA SAMI RAUNUKA WANNAN HARI MUTANEN HITILANE SUKA SHIRYASHI DOMIN YANA SASU CIKIN HALKAKA
CIKIN SHEKARAR 1945 RANAR 29 GA WATAN AFRIILU HITILA YAYI WASIYYAR KARSHE WACCE YA MUZANTA YAHUDAWA,SANNAN A WATANNE RUNDUNAR HITILA TA MIKA WUYA GA RUNDUNAR BARITANIYA A ITALIYA, SANNAN WASHE GARI WANI SOJA YA DAGA TUTAR SABIYAWA KAN WANI BENE DA BAIDA NISA DAGA GIDAN HITILA BAYAN HAKA DA KADAN SAI MUTANENSA SUKA JI WANI SAUTI YAFITO DA KARFI DAGA BAKINS ALAMAT YA HADIYE RANSA YA FADI MATTACE ,
ITA KUWA MATARSA SABODA BAKIN CIKI TA SHA GUBA TA BISHI ,
BAYAN HAKANE JAMUS SUKA MIKA WUYA MATAKI MATAKI,A ITALIYA AWATAN MAYU,DAGA NANNE KASASHEN TURAI SUKA KU BUTA DAGA HATSARIN HITILA AMMA SUNYI ASARAR RAYUKA DA DUKIYA WANDA BAZU KIDAYU CIKIN SAUKIBA.
NAKU
AUWAL MUHAMMAD ABDUL KADEER
DAN NAJERIYA A BIRNIN OMDURMAN SUDAN