Wani labari da na taba karantawa kan wani nasara da ya shiga mota zaiyi kaura ya bar garinsa , bayan motar ta dau hanya sai zumbur kamar ya tuna da wani abu , ya jawo jakarsa ya bude sai ya ciro rigarsa da wando da malafa {Hat}, yayi watsi da su ta tagar mota, mamaki ya game jama'ar cikin motarnan , suka kasa hakuri suka tambaye shi, sai yayi bayanin cewa ya kauracewa matarsa ne yana so ya sake sabuwar rayuwa don haka yake yasarda duk abunda zai sa ya iya tunawa da ita .
Abun da nake so nan mu fahimta shine mutum zaiso rabuwa da duk wani abunda zai tuna masa wani kunci ko matsi ko damuwa da ya taba shiga.
kamar yadda muka saba gani yayin da Allah ya budewa namiji kofofin arziki bayan ya shekara saba'in cikin talauci abunda zai fara yi shine zai tashi haikan don kauda duk abunda zai tuna masa da kwanakin talauci , don haka zai gina sabon gidan sama don kauracewa gidan kasa, ya sayi sabuwar mota don rabuwa da keke koma saiyada {sawu} ya auro sabuwar budurwa don ya bar matarsa ta fari uwar 'ya'yansa wacca suka zauna zaman hakuri da tawakkali ,
Wani mutum daya halarci wata liyafa da wani alhaji sabon kudi ya gaiyace shi yana cewa {{……bayan mun kammmala wannan liyafa wacca tana daga cikin manyan liyafofi dana taba halarta a rayuwata , abokan alhaji attajirai da 'yan siyasa suna masa bankwana da barka kan sabuwar budurwar amarya da yayi wanda shine sanadiyar wannan shagali , wasu ma sun ja motocinsu sun yi gaba sai ga wata mace marabanta da mabaraciya kadan ne tana kira ga alhazannan da su taimaketa su isar da sakonta zuwaga mai gidan , tana cewa itace matarsa shekaru arba'in da suka gabata saidai tun sanda ya fara samun kwangila a hukumar jiha da ma ta taraiya sai ya fara sauya salon mu'amala da ita , yana takalar fada don in ta mayar masa da martani ya sallame ta, hakan kuma akayi , ta kara da cewa yanzu haka wannan yaron da ke hanuna karamin dansa ne na zo karba masa hakkinsa amma masu gadi sun hana ni shiga , saboda basu santa ba, kuma dama bai taba yin masu gadi ba sai da Allah ya masa fatahi , don haka bazasu sanni ba, wannan mata ta karkare wannan bayani nata da wani matsakaicin kuka da tayi ta kokarin matse shi amma yaki . hawaye kuwa yana zuba car car daga idanunta , wasu daga cikinmu masu tausasan zukata suma suka kasa tsantsame hawayensu.}}
wannan dabi'a ta namiji yasa nayi shakkar matan aure suyi fatan Allah ya ya tarfa wa garin mazajensu nono, amma kai me ka/kika gani?