21.3.08

In 'yan Nijar shigen Nasara ne to 'yan Najeriya shigen yahudu ne !!!!!!!!

Ba shakka koyau kasuwa tau watse baturen mulkin mallaka yai riba matuka, haba jama'a daga sharhin littafi an koma muzgune-muzgune , wai har dan arewacin Najeriya zai zagi dan NIJAR ko akasin haka? !

In bamu yaudari kammu ba zamu gaya wa akammu gaskiya cewa kowace al'umma tana da hali irin nata , bayarbe yana da matukar kabilanci , bafillatani yana da kunya , inyamuri yana son kudi kamar yanda yake son 'ya'yansa koma fiye shi kuwa, shi kuwa bahaushe mai matacciyar zuciya ne , ta inda baisan yayi aiki mai kare mutunci ba shi dai ya samu jin dadin rayuwa da gaggawa , shan yanzu maganin yanzu , duk kuwa wanda yake so yasan waye bahaushe ya kamata yazo sudan , ya gani wallahi yahudun zamanin HITILA sun fisu kima , ga bara da roko da karuwanci da tsibbu da sata , abun mamaki har , wasu alhazaine ke dauko yara ta hanyar rudin iyayansu , su kawo su nan sudan suna bara , kuma dole kullun sai yaro ya kawo masa abunda zai daidai , da N5000 (dubu biyar) , in kuwa bai kawo daure shi za ayi da sarka a daki a tara masa gajiya , kuma ni bahaushe nace akwai yan najeriya akwai yan Nijer .
banga dalili da wani bahaushen Najeriya zaiwa dan nijer tinkaho dashi ba , Fetur ne ! amma ya zama kwalelenka , masu tsotsa nayi mu kuwa sai kallo a NTA .
Duk wanda yasan najeriya musamman kano jalla babbar Hausa yasan irin kaba'iran da akeyi wanda ya sabawa hankalin dan'adam , wanda ba dadin fadi wai ace har anyi bukin auren mace da mace a kano , ga wata matsalar ta 'yan luwadi a bauci , ina ganin manzon Allah cewa akai masa ya fara gargadi da iyalan sa na kusa , to shawarar da zan wa kowani marubuci kafin ya tsallaka ya dauko matsalolin kasashen waje ya fara da matsalolin Kanon da ba irin sabon Allah da babu ciki , karuwanci , bokanci , tsubbu, luwadi da madigo wanda muka sani da wanda bamu sai ba , sannan yayi kan wudil ko Bauci.

Galibi in ana maganar talaucin kasa ko tattalinnta to wannan zai sa mushiga batun siyasa da mahukunta , don ALLAH tambaya waya kashe Najeriya kudu da arewa in ba bahaushen arewa ba , waya saci dukiyar najeriya fiye dashi , waya kashe ilimi ? , bahaushe ne ! waya tattari kudi ya kai kasar waje ? , ba shakka batun da wani yayi kan cewa tun mutuwar Ahmadu Bello , komi ya lalace gaskiya ne !

Malam Dankwairo yana cewa :

yan arewa ga ranar sardauna
kuyi aniya yayan sardauna
kumai da himma ku dauke girma


to amma ina ! malam dankwairo ai daga mutuwar Gamji dankwarai wasu yan hausa fim suka dawo .
Bai taba halatta ga wani dan arewacin najeriya ya aibata wani a duniya ba , saboda dukkan aibi da abun kunya yana ga bahaushe musulmin najeriya , tunda a garin Abubakar tafawa balewa ne aka yi kisan kiyashi wa musulmai , akayi a jos , kafancan , zangon kataf , lantang a daidai lokacinda bahaushe ya kule wajen iya taka rawa da waka a hausa fim wanda ba abunda ya jawo face lalata yara manyan gobe , da sunan adabi , basu san duk adabin da ba ladabi shirme bane .
Don ALLAH ka fadi mun in bahaushe bai hana kashe dan'uwansa musulmi a arewa ba to me zaiyi in ana kashe a kasar inyamurai , idan har wai wasu zasu ce Nijer jahila ce to ai suna da uzuri , mu masana meye uzurinmu ?
ya kamata mu gane dalilin da Allah yafi fushi da yahudu fiye da nasara , su yahudu suna da matukar ilimi amma sukai fatali sanin da Allah ya basu , sukai ta bin son zuciya shi yasa Allah yace musu " magdhubi alaihim" wato wadanda akai fushi dasu, su kuma nasara jahilai ya kira su da " Addhaleen" wato batattu.

wani abu da nake so jama'a su fahimta shine , tun zamanin juyin faransa wato (french revolution) har yau ba kasar duniya da ta bawa mace 'yanci ko hakki, tunda a mahaifar juyin faransa aka hana mata musulmai sa hijabi , ko su ba mata bane? , kai a BAUCI nasan makarantar da har yau mace bata da damar sa hijabi , kuma bari mugani zamu tabbatar cewa akwai hakkin mace idan Hillary Clinton taci zabe a amurka dukda cewa , jamiyar jamhuriya ta bush ta sanya amurka a bala'i don haka ba'a tsammanin wani zai zabi wannan shu'umar jam'iya, dukda cewa Barrack Obama baki ne , sannan ubansa musulmi ne , sannan ita clinton tana da uwa a murhu tunda mijinta yayi zaman farin gida ita kuwa ba lokon da bata sani ba, to ku marubutan hausawa idan har taci nasarar zama shugaba to na yarda akwai wani a abu a wayewar bature mai suna 'yancin mace .

shin 'yan'uwa kunsan 'yancin mace ga yammacin duniya ?

to in baku sani ba shine karuwanci da tallace-tallacen a gidan talabijin , saboda in har aka yarda aka nuna mata 'yan cinta kamar yadda musulunci ya nuna to fa mazinata maza sun shiga uku don baza su sami nishadantuwa dasu ba , saboda zasu yi aure kuma ba wawan da zai yarda ya auri mace wani ya ringa masa yankan baya , don haka ni ba mace uwa , kanwa , ya , kaka ba , ko kiyashi ne aka zalunta ina goyon bayan ya nemi hakkinsa , amma ta yaya ? ? ?

finafinan hausa ma jawabi ne , mai hankali ke ganewa !!!!!

Naku Alkalami