10.4.08

Hukumar Iran ta zartar da hukuncin kisa kan malaman sunnah har lahira

Daga cikin muzgunawa da hukumar iran ta ke wa ahlussunah , kullum
ana ganin sabon abun ban mamaki gashi kwanannan ta halaka sheikh Abdul
Kuddus mulazihi da sheikh Muhammad yusuf sahraby bayan an gurfana dasu
a kotu (mahakama) r garin Zahedan , shi dai malam Abdulkuddus
shine shugaban wata makaranta mai suna Darul furkan a birnin Iranshahr
dake yankin Bulushistan .
An kame malaman ne bayan musayar wuta tsakanin sojojin hukuma da
dakarun Jundullahi.
kamar yadda kafar sadarwa ta Ahlussan na Iran tayi bayani cewa
dakarun hukuma ta bisne su ba tare da mika gawauwakinsu ga iyalansu ko
yan'uwansu Ahlussunna ba.
A gefe guda kuma an gurfanar da limami mai huduba a masallacin
Ahlussunnah a garin Azad-shahr , an gurfanar da shine da laifin fito
na fito da hukuma , da kushe malaman mazhabin shi'a kan cin mutuncin
daukacin sahabban manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gareshi da uwar muminai A'isha Allah ya kara mata yarda , da
kuma laifin hana jama'a ziyartar hubbaren shehunan shi'a don
neman tabarruki .
fassara daga :
http://www.islammemo.cc/akhbar/arab/2008/04/10/62249.html