21.3.08

In 'yan Nijar shigen Nasara ne to 'yan Najeriya shigen yahudu ne !!!!!!!!

Ba shakka koyau kasuwa tau watse baturen mulkin mallaka yai riba matuka, haba jama'a daga sharhin littafi an koma muzgune-muzgune , wai har dan arewacin Najeriya zai zagi dan NIJAR ko akasin haka? !

In bamu yaudari kammu ba zamu gaya wa akammu gaskiya cewa kowace al'umma tana da hali irin nata , bayarbe yana da matukar kabilanci , bafillatani yana da kunya , inyamuri yana son kudi kamar yanda yake son 'ya'yansa koma fiye shi kuwa, shi kuwa bahaushe mai matacciyar zuciya ne , ta inda baisan yayi aiki mai kare mutunci ba shi dai ya samu jin dadin rayuwa da gaggawa , shan yanzu maganin yanzu , duk kuwa wanda yake so yasan waye bahaushe ya kamata yazo sudan , ya gani wallahi yahudun zamanin HITILA sun fisu kima , ga bara da roko da karuwanci da tsibbu da sata , abun mamaki har , wasu alhazaine ke dauko yara ta hanyar rudin iyayansu , su kawo su nan sudan suna bara , kuma dole kullun sai yaro ya kawo masa abunda zai daidai , da N5000 (dubu biyar) , in kuwa bai kawo daure shi za ayi da sarka a daki a tara masa gajiya , kuma ni bahaushe nace akwai yan najeriya akwai yan Nijer .
banga dalili da wani bahaushen Najeriya zaiwa dan nijer tinkaho dashi ba , Fetur ne ! amma ya zama kwalelenka , masu tsotsa nayi mu kuwa sai kallo a NTA .
Duk wanda yasan najeriya musamman kano jalla babbar Hausa yasan irin kaba'iran da akeyi wanda ya sabawa hankalin dan'adam , wanda ba dadin fadi wai ace har anyi bukin auren mace da mace a kano , ga wata matsalar ta 'yan luwadi a bauci , ina ganin manzon Allah cewa akai masa ya fara gargadi da iyalan sa na kusa , to shawarar da zan wa kowani marubuci kafin ya tsallaka ya dauko matsalolin kasashen waje ya fara da matsalolin Kanon da ba irin sabon Allah da babu ciki , karuwanci , bokanci , tsubbu, luwadi da madigo wanda muka sani da wanda bamu sai ba , sannan yayi kan wudil ko Bauci.

Galibi in ana maganar talaucin kasa ko tattalinnta to wannan zai sa mushiga batun siyasa da mahukunta , don ALLAH tambaya waya kashe Najeriya kudu da arewa in ba bahaushen arewa ba , waya saci dukiyar najeriya fiye dashi , waya kashe ilimi ? , bahaushe ne ! waya tattari kudi ya kai kasar waje ? , ba shakka batun da wani yayi kan cewa tun mutuwar Ahmadu Bello , komi ya lalace gaskiya ne !

Malam Dankwairo yana cewa :

yan arewa ga ranar sardauna
kuyi aniya yayan sardauna
kumai da himma ku dauke girma


to amma ina ! malam dankwairo ai daga mutuwar Gamji dankwarai wasu yan hausa fim suka dawo .
Bai taba halatta ga wani dan arewacin najeriya ya aibata wani a duniya ba , saboda dukkan aibi da abun kunya yana ga bahaushe musulmin najeriya , tunda a garin Abubakar tafawa balewa ne aka yi kisan kiyashi wa musulmai , akayi a jos , kafancan , zangon kataf , lantang a daidai lokacinda bahaushe ya kule wajen iya taka rawa da waka a hausa fim wanda ba abunda ya jawo face lalata yara manyan gobe , da sunan adabi , basu san duk adabin da ba ladabi shirme bane .
Don ALLAH ka fadi mun in bahaushe bai hana kashe dan'uwansa musulmi a arewa ba to me zaiyi in ana kashe a kasar inyamurai , idan har wai wasu zasu ce Nijer jahila ce to ai suna da uzuri , mu masana meye uzurinmu ?
ya kamata mu gane dalilin da Allah yafi fushi da yahudu fiye da nasara , su yahudu suna da matukar ilimi amma sukai fatali sanin da Allah ya basu , sukai ta bin son zuciya shi yasa Allah yace musu " magdhubi alaihim" wato wadanda akai fushi dasu, su kuma nasara jahilai ya kira su da " Addhaleen" wato batattu.

wani abu da nake so jama'a su fahimta shine , tun zamanin juyin faransa wato (french revolution) har yau ba kasar duniya da ta bawa mace 'yanci ko hakki, tunda a mahaifar juyin faransa aka hana mata musulmai sa hijabi , ko su ba mata bane? , kai a BAUCI nasan makarantar da har yau mace bata da damar sa hijabi , kuma bari mugani zamu tabbatar cewa akwai hakkin mace idan Hillary Clinton taci zabe a amurka dukda cewa , jamiyar jamhuriya ta bush ta sanya amurka a bala'i don haka ba'a tsammanin wani zai zabi wannan shu'umar jam'iya, dukda cewa Barrack Obama baki ne , sannan ubansa musulmi ne , sannan ita clinton tana da uwa a murhu tunda mijinta yayi zaman farin gida ita kuwa ba lokon da bata sani ba, to ku marubutan hausawa idan har taci nasarar zama shugaba to na yarda akwai wani a abu a wayewar bature mai suna 'yancin mace .

shin 'yan'uwa kunsan 'yancin mace ga yammacin duniya ?

to in baku sani ba shine karuwanci da tallace-tallacen a gidan talabijin , saboda in har aka yarda aka nuna mata 'yan cinta kamar yadda musulunci ya nuna to fa mazinata maza sun shiga uku don baza su sami nishadantuwa dasu ba , saboda zasu yi aure kuma ba wawan da zai yarda ya auri mace wani ya ringa masa yankan baya , don haka ni ba mace uwa , kanwa , ya , kaka ba , ko kiyashi ne aka zalunta ina goyon bayan ya nemi hakkinsa , amma ta yaya ? ? ?

finafinan hausa ma jawabi ne , mai hankali ke ganewa !!!!!

Naku Alkalami

7.2.08

Shi wannan ba ta'addanci bane

Ba shakka satar yaran dafur da wata kungiyar jinkai ta faransa tayi ya wuce a kafofin watsa labarai kamar shafa labari shuni amma ba shakka ga dukkan mai hankali wannan abu zai saura a tunaninsa har sai ya fahimci meye ma'anar ta'addanci a fahimtar yammacin duniya
Ba shakka wannan nasaran da Allah ya jarrabi dan afurka dashi bai dakatar da mulkin mallaka ko bautar da bakin fata ba kamar yadda wasu suke cewa ai ya koma bautar da hankulan bakin mutun ne to har yanzu suna da abun da suke kira White slavery in zai yuyu a hausa muce farar bauta wacca wannan satar yara daga dafur da chadi yana daga ciki hakan kuma sun yi shi ne domin 1 karuwantar da su 2 kiristar da su 3 yanke musu wasu gabobi domin bawa turawa mara sa lafiya,kamar koda, to don Allah ina jinkai da mutantakar da Allah ya saka a zuciyar duk wani abu mai rai idan ya zama dan afurka musulmi ba masa kallon cikakken mutum innama shi dan adan a mataki na biyu.

Wannan mas'ala kuwa ta wuce mai tambayarta tun lokacin da shugaban faransa ya zo yayi kutun-kutun ya sa aka saki wadannan masu laifin wanda Wannan waki'a ta baiyana gaskiyar masu cewa wadannan kungiyoyin jinkai na yammacin duniya suna da ajandodi boyaiyu ba wai nufinsu shine jin kai ba

In bamu mance ba yammacin duniya sunyi ruwa sunyi tsaki wajen rufe wasu kungiyoyin musulunci da rufe musu asusun bankunansu wai suna tallafawa ta addanci, sannan suke hana gungiyoyin jinkai na musulunci wuraren da bala'I ya dauka musu don su kiristartar da wanda suka so ba tare da ja'inja ba

6.2.08

ALLAH JIKAN MALAM BAKAR ABU ZAID


Malam bakar abu zaid ya rasu ranar talata 25/1/1429 h wanda yayi daidai da 5 / 2 / 2008m an haife shi ne kuwa 1365h .
sheikh Ahmad [mijin yarsa ] shine ya jagoranci masa salla kamar yanda malam bakar yayi wasici , sallar kuwa ta sami halartar sheikh Abdul-Aziz bn Abdallah Ali sheikh da sarakuna da dalibai da masoyan malamin , hat tituna da hanyoyi suha cika saboda jama'ar da suka kai gawarsa har makabartar Dir'iyah .


Malamin ya fito ne daga gidan mutunci da dukiya , yayi karatun allo sannan ya shiga firamare , ya sami karasa karatunsa tun daga wani bangare na karatunsa na firamare sannan ma'ahad ilmy da sannan tsankayar karatun shari'a da babbab makarantar alkalanci a birnin Riyadh , a gefe guda kuma yana gurfana gaban shehunnan malamai don neman ilimi a zaurukansu , ya karanci luga ga malam salih bn Abdullahi bn mutlaq tsohon alkali a Riyadh har saida ya hardace makamomi ashirin da biyar daga makamakamatul hariry da sharhinsu na Abul Abbas assharbashi a gabansa.

sannan ya lizimci sheikh Abdul-Aziz bn baz [ Allah ya rahanceshi] ya karanci abubuwa da dama a gunsa daga ciki hadda bangaren aikin hajji da cikin littafin Almuntaqa a masallacin makkah , sannan ya dau ilimi gun malam muhammad al-amin asshanqidy inda ya karanci tafsirinsa adwa'ul bayan da juzu'i na farko a cikin littafin labbun bincike da jayaiya da usulul fikhi da ilimin dangi a massallacin madinah da gidansa.
An nada shi alkali a babban kotun madina ya zama malami a masallacin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi bayan haka da shekara daya ya zama wakili a ma'iakatar shari'a [ ministry of justice] , ya kuma zama jakadan sa'udiya a majma'in fikihu na kungiyar hadin kan duniyar musulunci, yana cikin dauwamammen komiti na bincike da fatawa.
Lokacin da yake alkalanci ne ya ci gaba da karatu daga nesa har ya same shaidar masta da dakta .
malam bakar abu zaid ya wallafa littatafai kamar hamsi an buga wasu daga ciki akwai


1-ابن القيم . حياته ، وآثاره ، وموارده .
2 – التقريب لعلوم ابن القيم .
3 – فقه النوازل . مجلدان .
4 – معجم المناهي اللفظية .
5 – طبقات النسابين .
6 – معرفة النسخ الحديثية .
7 – التحديث فيما لا يصح فيه حديث .
8 – حلية طالب العلم .
9 – التعالم .
10 – الرقابة على التراث .
11 – تعريب الألقاب العلمية .
12 – آداب طالب الحديث من الجامع للخطيب .
13 – التراجم الذاتية من العزاب والعلماء وغيرهم .
14 – تسمية المولود .
15 – عقيدة ابن أبي زيد القيراوني والرد على من خالفها .
16 – تصنيف الناس بين الظن واليقين .
17 – حكم الانتماء .
18 – هجر المبتدع .
19 – التحذير من مختصرات الصابوني في التفسير .
20 – براءة أهل السنة من الواقع في علماء الأمة .
21 – خصائص جزيرة العرب .
22 – جزء في مسح الوجه باليدين بعد الدعاء .
23 – جزء في زيارة النساء للقبور .
24 – بدع القراء .
25 – لا جديد في أحكام الصلاة .
26 – تحقيق كتاب " الجد الحثيث في بيان ما ليس بحديث " للعامري .
27 – تحقيق اختيارات ابن تيمية للبرهان ابن القيم .
28 – أذكار طرفي النهار .
29 – تحريف النصوص .
30 – المثامنة في العقار .
31 – آداب الهاتف .
32 – أدب الثوب والأزرة .


16.1.08

SHIN MATA ZA SUYI FATAN DUKIYA GA MAZAJENSU KUWA?



Wani labari da na taba karantawa kan wani nasara da ya shiga mota zaiyi kaura ya bar garinsa , bayan motar ta dau hanya sai zumbur kamar ya tuna da wani abu , ya jawo jakarsa ya bude sai ya ciro rigarsa da wando da malafa {Hat}, yayi watsi da su ta tagar mota, mamaki ya game jama'ar cikin motarnan , suka kasa hakuri suka tambaye shi, sai yayi bayanin cewa ya kauracewa matarsa ne yana so ya sake sabuwar rayuwa don haka yake yasarda duk abunda zai sa ya iya tunawa da ita .

Abun da nake so nan mu fahimta shine mutum zaiso rabuwa da duk wani abunda zai tuna masa wani kunci ko matsi ko damuwa da ya taba shiga.


To amma wani abu shine mace zata iya zama abun da za'a yasar don kar a tuna da wani yanayi da aka taba shiga na kunci musammam talauci kamar yadda wancan Nasara ya zubar da tufafinsa kuma dama Allah ta'ala cikin kurani ya kira su tufafi inda yacewa maza : [[ su tafafi ne a gareku , kuma kuma tufafine a garesu ]] suratul bakarah , ayata 187.

kamar yadda muka saba gani yayin da Allah ya budewa namiji kofofin arziki bayan ya shekara saba'in cikin talauci abunda zai fara yi shine zai tashi haikan don kauda duk abunda zai tuna masa da kwanakin talauci , don haka zai gina sabon gidan sama don kauracewa gidan kasa, ya sayi sabuwar mota don rabuwa da keke koma saiyada {sawu} ya auro sabuwar budurwa don ya bar matarsa ta fari uwar 'ya'yansa wacca suka zauna zaman hakuri da tawakkali ,

Wani mutum daya halarci wata liyafa da wani alhaji sabon kudi ya gaiyace shi yana cewa {{……bayan mun kammmala wannan liyafa wacca tana daga cikin manyan liyafofi dana taba halarta a rayuwata , abokan alhaji attajirai da 'yan siyasa suna masa bankwana da barka kan sabuwar budurwar amarya da yayi wanda shine sanadiyar wannan shagali , wasu ma sun ja motocinsu sun yi gaba sai ga wata mace marabanta da mabaraciya kadan ne tana kira ga alhazannan da su taimaketa su isar da sakonta zuwaga mai gidan , tana cewa itace matarsa shekaru arba'in da suka gabata saidai tun sanda ya fara samun kwangila a hukumar jiha da ma ta taraiya sai ya fara sauya salon mu'amala da ita , yana takalar fada don in ta mayar masa da martani ya sallame ta, hakan kuma akayi , ta kara da cewa yanzu haka wannan yaron da ke hanuna karamin dansa ne na zo karba masa hakkinsa amma masu gadi sun hana ni shiga , saboda basu santa ba, kuma dama bai taba yin masu gadi ba sai da Allah ya masa fatahi , don haka bazasu sanni ba, wannan mata ta karkare wannan bayani nata da wani matsakaicin kuka da tayi ta kokarin matse shi amma yaki . hawaye kuwa yana zuba car car daga idanunta , wasu daga cikinmu masu tausasan zukata suma suka kasa tsantsame hawayensu.}}

wannan dabi'a ta namiji yasa nayi shakkar matan aure suyi fatan Allah ya ya tarfa wa garin mazajensu nono, amma kai me ka/kika gani?


6.1.08

BENAZIR BHUTO DA GUNKIN DABINO


Bilawal Bhutto dauke da hoton marigayiyar


Sau da dama wannan zamani yana kawo wasu wakoki da ake rerawa da har yanzu wasu wanda ni ma Alkalami ina daga cikinsu mun kasa gane hakikanin ma'anarsu , mu samman wakar nan ta Dimukuradiya wanda na hakikance cewa kidine kawai akeyi ake rausayawa , amma ba wata kalma ko jumla ciki bare a fahinci manufarta.

ku yafeni ya ku mabuga tamburan dimukuradiya in abun bai muku dadi ba , amma yadda ya wajaba in nunfasa haka kuma ya wajaba in baiyana irin wannan rainin hankalin da nake ji a cikin kade kaden dimukuradiya .

Allah yayi cikawa wa malama Benazir Bhutto tsohuwar firayim minista kuma 'ya ga tsohon firayim minista Zulfikar Ali Bhutto wanda ita da mahaifinnanta duk mabiya tafarkin shi'a ne , a yanzu dai ana kokarin ganin binciko wadanda suka yi wannan buruntu, inda shugaba Pervez Musharraf ya daura alhakin wannan kisan gillan ga Alka'ida saboda ita bhutto ta sha lasan takobin murkushe an alka'idan , sannan kuma suna ganin itace takeda cikakken goyon bayan amurka da yan barandanta fiye da kowa a pakistan saboda shi musharraf namiji ne kuma soja don haka akan samu tangarda dashi , baya bi a makance , sannan a bangare guda kuma za'a iya tuhumar shi musharraf din saboda jagorancin da take yi na kokarin kadashi a zabe mai zuwa.

Abunda ya ja hankalina kan wannan waki'a shine yanda dimukradiya ta dawo gunkin da akayi shi da dabino , in aka koshi ayi masa sujjada in kuma aka ji yunwa a ringa gutsura anaci , ta inda ita bhutto ta bar wasiyar a daura danta Bilawal Bhutto dan shekara 19 wanda yake karatun tarihi a jami'ar Oxford kan karagar jam'iyar Parkistan People Party { PPP} , wanda shine kenan zai fito takara da Musharraf , shi kuma mahaifinsa Asif Ali Zardar mataimakinsa. haka nan shugaba Gaddafi {dukda cewa shi ba kan tsarin dimukuradiya yake ba , amma jamhuriya ne ba mulukiya ba} yana neman daura dansa Saiful-islam kan mulki bayansa , haka ma shugaban masar mubarak nufinsa kenan, marigayi Hafez Asad shima ya daura dansa Basshar Al-asad a Syria .

Abun mamaki jaridar Almizan dangane mulukiyar Benazir Bhutto cewa tayi :

''
A yayin da kasashen duniya ke ta kiraye-kirayen a samar da wani kwamitin bincike na kasa-kasa da zai binciki masu hannu a harin da aka yi wa Bhutto, tuni har jam’iyyarta ta zabi danta da mijinta a matsayin wadanda za su ci gaba da jan ragamar jam’iyyar don fuskanta zaben da ke tafe ''.
zaka iya karanta wannan rahoto nasu a yanar gizo ta wannan adreshi http://www.almizan.net/bls803c.html, alhali kuwa shafin yanar gizo na malama Bhutto ya tabbatar cewa gadar wa danta da mahaifinsa tayi in da ya baiyana cewa :

'' Benazir Bhutto's 19-year old son has been appointed chairman of his late mother's opposition political party in Pakistan.

Bilawal Bhutto, who is reading history at Oxford, will chair the Pakistan People's Party with his father, Asif Ali Zardar, as co-chairman.

Bilawal Bhutto right, being comforted by his father Asif Ali Zardar. Party officials made the announcement after the reading of Miss Bhutto's will following her assassination last week.'' , za kuma a sami wannan a cikin shafinta mai adreshin http://www.benazirbhutto.co.uk/Default.php

to abun tambaya ko me yasa yan shi'an basa so ace gadarwa tayi , Allahu a'alamu!


wannan na nuna cewa yanzu ma'anar dimukuradiya ya tashi daga hukumar jama'a zuwa hukumar gado kuma koda magajin karami ne dan shekara shata tara .

wannan bazai bada mamaki sosai ba idan muka tuna cewa Amurka su suka fara taya Moi Kibaki murnar komawa kan mulki dukda sun san cewa bashi ya lashe zabenba , amma tunda sunsan ba dole ne Odinga ya sake musu kamar yadda kibaki yabari suka ringa diban musulmai suna kaiwa Gwantanamo ba da sunan ta'addanci, sannan baza mu mance cewa Hamaz suka ci zaben palasdinu ba, amma turai gaba daya suka juya musu baya suka ringa azabtar da jama'ar da yunwa saboda basu zabi wadanda su { turai } suke so ba wato Fatah .
Allah yayi gaskiya da yace '' yahudu da Nasara basu yarda da kaiba harsai kabi tafarkinsu ''



17.12.07

HAPPY EID -UL- ADHA

8.12.07

WALIDAINI

Ina zaune karkashin inuwar la'asariya , duk damuwata wata ya kusa faduwa gashi ban sa wani rubutu da yake matsayin abinci ga BLOG dina kamar yadda nasara suka kira shi , ko MUDAUWANA inji larabawa adaidai lokacinda naga wani bahaushen ya ambaceshi TURAKA , wanda ni tawa turakar na mata inkiya da ALKALAMI saboda na fahimci zamanin tsinin mashi, ko kibiya, ko roka , ko allura ya gushe yanzu lokacine na tsinin alkalami.

Ina cikin murza alkalamina a tsakanin hakora don tuna guzurin da zan kawo wa masu sai ga wani abokina sa'idu yana tafiya jikinsa a mace kamar bai da laka duk ayoyin bakin ciki suna karantuwa a fuskarsa kai harma da surori.

Saidu lafiya kuwa kake tafe kana raba hanya kamar kasha ruwan bagaja ?
na kamo hanunsa na zaunar dashi kan dakalin gidanmu

'' ai ka bari kawai dama giya nasha ai da da sauki don kuwa cutarta daga ni sai ni''

to me ya faru me ka rasa bayan kana karbar albashin da bai gaza dubu arbain ba.
Bayan dogon rarrashi sai ya kada baki yace :

"Mahaifiyata ta rikeni a cikinta tsawon wata tara, jininta yana gudana tare da jinina , harna zame mata tamkar wata gaba daga jikinta, sannan ta zaroni daga cikinta kamar tana zaro ranta , da na sauko duniya kuwa ba abunda ke sata murmushu kamar murmushina , kamar yadda ba abu mai sata kuka kamar kukana, ta bani nonota na tsotsi rayuwata daga cikinsa, yayinda kuwa nayi zazzabin hudowar hakori sai barci ya kaurace masa ta kuma mance dandanon abinci, ta hana kanta dadadan abubuwa domin ta bani , ta yunwata domin in koshi, kai Alkalami ba abunda nake tunawa kamar randa ta kwashi uwar jari da ribar kulikulinta ta saya mun adaka da garin rogo da sukari da tsintsiya da fartanya zan tafi makarantar kwana , ita kuwa ta zauna hanu banza , nazo tafiya tana hawaye wai don zan gamu da yaran masu hanu da shuni ana kawo musu ziyara a motocin alfarma , a kawo musu madara da biskit da kanzon kwali dama abunda banji ba, ban taba gani ba, ban kuma taba darsa shi a tunaniba.

Shiko mahaifina bai tada fashin zuwa jeji ba komai sanyi komi zafi , tun hantsi kuwa in ya riki gatari sallar azahar ce ke sa ya saki, ya debo abun da ya samu , ya dawo gida kewaye da abubuwa uku yunwa da kishi da gajiya, amma ba abunda zai tarwatsa masa kan wannan musallasi sai sautina yayin da nace OYOYO BABA ! nayi watsi da wasan da nake yi na sheko da gudu shi kuma ya daga ni sama ya jijjiga cikin farin ciki.

Lokacin da na gama makaranta da sakamakon da ya ban damar shiga jami'a gashi lamari ne mai bukatar kudi, gonarsa ta kusa da makabarta ya sayar don biya mun abunda ya jawo masa zagi da zunde da kifce da yafuce a kauyemmu cewa ga wanda ya tozarta NA DUKE TOSHON CINIKI don dansa yayi karatun nasara asarar duniya, wasu ma har .......""

Nan take na katseshi nace : " sa'idu wai meye alakar wannan dogon jawabi da damuwarka , ai falalar iyaye abune a baiyane kamar wata daren sha hudu , da zaka ji wahalar da iyayena suka sha kaina da baka iya hana hawaye tsirarowa da idanunka ba, shi yasa nake musu carafken kwai kan kanfa."

Saidu ya ce '' ai in gaya maka ban taba jin kwakwalwa a kaina ba saida na ganni a kotu ''

Nan take nayi zumbur nace '' me ya kaika kotu? wa ya maka kazafi ? yanzu a garinnan har an fara yiwa mumunai kage? ''

Sa'idu yace '' mahaifana nane suka kaini gaban alkali don ya karba musu hakkinsu , saboda basu da karfin yin aikin karfi kuma gashi suna bukatar abunda zasu ci''

nace '' to ina makudan albashin da kake karda daga bankin al'umma ? ina suke tafiya? "

yace yanzu " yanzu Alkalami ka mance yanda muke da Biba , yariyar nan kamar ta daure ni da guru "
Nace " A'a ka daure kanka dai, yo imma da hanun boka ta daure ka , ina Aayatul kursiyu da kula'uzai ? "

Ya kara da cewa" ai in gaya maka in har na damki kudin nan bana iya zarcewa ko ina sai gidansu Biba, in damka mata tayi kasafin wannan wata , ta yafuta mun kadan da zanci garau-garau"

Yaci gaba da cewa yanzu haka alkali yadaga sauraran karar zuwa mako mai zuwa , so nake inje in roke su su janye karar , in nemi gafarar su, amma fa kar ka gayawa kowa , don na sanka"

Nace :" in banda kai ka taba ji Alkalami tona asiri ? "


26.10.07

BIBIYAR LITTAFIN ‘’SUDA’’

15/shauwal/ -h _26/11/2007

Malam Kabiru Yakasai ba shakka haziki ne mai matukar hikima , da alama kuwa hannunsa ya jima yana goga alkalami kan takarda .
Duk wannan takaitaccen yabon ba wai nasan shi bane , saidai na kwatanta zakakurancinsa ne sakamakon karanta littafinsa mai suna ‘’suda’’ littafinda ya hada nishadantarwa da tarbiya da azanci .

Shekaran jiya nake karanta shi lokacinda na bakonci dangina a omdurman na jamhuriyar sudan , amma lokaci zuwa lokaci sai in kyalkyale da dariya saboda in nayi hakuri a taran aradu da kan dankani wani lokaci to wani lokacin kuma bazan iya hana bakina ‘yancin dariya ba.

Mun kasance muna kishirwan mawallafa irin malam Kabiru ruwan wankin daudar zamantakewa , don kuwa mun kosa da masu kwashe baiwar talifi da Allah ta’ala ya musu sui ta yawo tsakanin so da ki , da soyaiya da kiyaiya kamar mu hausawa wata al’umma ce wacca bata da wata matsala sai soyaiya .

Malam ya fara bada labarin baba suda a takaice wanda shi kuma shine ya ba yara labarin rigingimun dankane, kuma ni a fahimta ta malam ya nusar damu ne cewa tara yara da basu labaru wata hanyace ta tarbiya , kamar yadda Allah ta'ala ya dauki wannan salo a kaso mai girma na Alkur’ni kamar : suratu Yusufa kacokam dinta ta bada labarin annanbi yusufa ne , ta kuma bada mahimmanci kan al’amuran zamantakewa ,wasu surori kuma annabi Isa , Musa , Dauda da Sulaiman , Ibrahin da sauransu , da labarin sarakuna kamar Fir’auna da Lamarudu , duk wannan domin mu dau izna .

Wani abu mai tabbatar mana cewa mawallafin ya na da hadafin azo agani wajen talifin wannan littafin shine inda yayi bayanin cewa baba suda ya bawa yara wannan labarin ne saboda ya umurci wani yaro da ya sai wa alkaki da ya samma dan’uwansa da ya makara bai samu ba , sai yaron yaki daga nan sai ya kwabe su da su bar rowa daga nan ya fara basu labarun wahalhalun da dankane ya sha wanda galibinsu sakamakon rowarsa da son kudinsa ne kamar dan canjin yahudawa.
Mawallafin yayi bulala wa sharifan karya dama na gaske masu ci da salsalar nasaba , yan danfara , barayin zaune , sannan yayi bayanin yadda dankane ya tashi daga almajiri zuwa matsayin alkali zuwa waziri har sanda yayi juyin mulki ya dawo sarki mai cikkakken iko daga nan kuma yayi karkon kifi ya koma tunku , abun mamaki!! .

Sannan yaci gaba da tsumage ‘yandaudu da malaman tsubbu 'yan kawo rago kawo zakara mai kwai, da masu ruwan ido , har lokacinda dankane ya ga ba harkar da bai shiga ba amma bai ci nasara ba saura masa harka daya da bai jarraba ba itace harkar kamun kai da bin addini sauda kafa , daga nan ya yasar da duk wani shashanci har ma ya koma alaramma mai jan baki a ramalana.

Saidai malam kabiru abunda ya daure mun kai wai shin akwai wani nassi daga kur’ani ko hadisi mai tabbatar da cewa sharu wuta bata kama shi koko dai siddabaru da rufa ido sharifan suke yi ? .
Har wayau aganina ba kai tsaye ba ka daurewa bokaye da malaman tsubbu gindi in da kayi bayanin wani malami mai gudun duniya ya ba dankane wuridin kiran aljanu to amma wannan malamin ba kamar yanda kayi bayani cewa malamin Allah da annabi bane tunda wannan shirka ne hada Allah da wani ne , Allah kuwa yana cewa ‘’ idan bayina suka tambayeka dangane da ni to ni a kusa nake ina amsa kiran mai kira in ya kirani ’’

Wani abun da na lura dashi kan littafin ‘‘ suda‘‘ shine jama’a sunfi saninsa da ‘‘Dankane‘‘ , sai naga dama malam kabiru ya rada wa littafin Suna DANKANE , sannan kalmar dankane wani sa’in malam yakan sa mata wasalin [e] wani lokaci kuma wasalin {I} tsammanina so yake ya nusar da mu cewa duka hausa ce karbabbiya dankani da dankane.
Zanso ku karanta littafin SUDA sai dai kar ku zargi malam kabiru idan bakin ku ya barke don dariya.
Wassalam.

5.10.07

BIBIYAR YAKIN DUNIYA NA BIYU


A LOKACINDA JAMUS TA YAKI POLAND ,A WATAN SATUMBA 1939 ,SHEKARA ASHIRIN BAYAN YAKI DUNIYA NA DAYA , HAR ANYI TSAMMANIN ZAMAN LAFIYA YA DAWWAMA, SAI GASHI, ANGULU TA KOMA GIDANTA NA TSAMIYA, SABODA JAMUS DA JAPAN SUNYI KOKARIN BAZA MULKINSU HAR KASASHEN TURAI DA AFRICA

DA GABAS TA TSAKIYA SAIDAI SOJOJIN HADIN GWIWA SUN FAR MUSU BAYAN SUN BIYA WASU BUKATUNSU BANDA WASU ,MASU KIDAYA SUNA CEWA RAYIN MUTUM DUBU HAMSINNE YA FITA TA INDA WASU SUKACE BA A SAN YAWANSUBA.
DA GA CIKIN WAKI OIN DA ZAN IYA TUINAWA SHINE YAKINDAI YUAFARANE WATAN SATUMBA 1939 ,WATAN AFRILU HITILA ,YAYI KAFAR ANGULU GA YARJEJENIYAR SHEKARAR 1939 TSAKANINSA DA BARITANIYA, SANNANN WATAN AGUSTA NAZI TA KULLA YARJEJENIYA ZAMAN LAFIYA DA SABIYAWA SHE KUWA HITILA YAYI HAKANE DOMIN KADA RASHA TACE UFFAN,YAYIN DA ZE KAIWA POLLAN HARI,WATO HARIN DAYA KAI MATA A SATUMBA SANNAN DAGA CIKIN TUN AWA A WATAN AFRILU 1940
JAMUS TA AUKAWA DENMARK, TA INDA DA KEWAYE IYA KOKINTA ITA KUMA DENMARK TA MIKA WUYA .
A KUMA WATAN MAYU JAMUS TA KEWAYE BELGIKA A GEFE GUDA KUMA FARANSA DA BARITANIYA SUNYI KOKARIN SHIGOWA BELGIKA SAI JAMUS TA FARMUSU ,,SANNAN JAMUS TA KAMA AREWACIN FARANSA CIKIN SAUKI ABINDA YABASU MAMAKI, HAR SUKA DAKATA DA DOMAIN KARA SHIRI FARANSA DA RUNDUNARTA NAN TAKE TAFRAS MUSU/
SANNAN A WATAN YULI, JAMUS TA KEWAYE FARISA ,KUMA TA KEWAYE TSUBURIN CHANEL, A WATA MAI ZUWA KUMA HITILA YA UMARCI RUNDUNARSA DA AUKAWA BARITANIYA
WATA BABBAR WAKIM A KUMA ITACE HARE HAREN SAMA MASU GIRMA WANDA JAMUS TA ZAZZAGE A BIRNIN LONDON,ITAMA LONDON DA DAU FANSA WANDA BAIKAI NA JAMUS BA.
CIKIN SHEKARAR 1941 WATAN YULI,KWATSAM SAI YARJEJENIYAR TSAGAITA KAWO HARI,TA KARE TSAKANIN JAMUS DA SABIYAWA,YAYINDA JAMUS TAKAI MUMMNAN HARINDA TARIHI YA BUGA MASA HATIMI.
SANNAN CIKIN SHEKARAR 1942 WATAN NUWAMBA JAMUS TA MAMAYE KUDANCIN FARANSA DOMIN SU KAMA JIRAGEN RUWANSU SAI DAI FARANSA TA KONA DOMIN KADA YA KOMA ABOKAN GABA.
SANNAN CIKIN SHEKARAR 1934 WATAN AFRILU BARITANIYA TA YAUDARI JAMUS YAU DARAR DA TA BADA MAMAKI TA YANDA SUKA SANYA TAKARDA MAI NUNA CEWA ZASU YAKI WURARE GUDA BIYU A GIRKA, SANNAN SUKA YASAR A GEFAN TEKUN ANDALUS TAYANDA JAMUS ZASU TSUNTA AMMA SU SUNA SONE SUKAI HARI SICILY DOMIN KADA JAMUS SU FAR MUSU DON HAKA JAMUS TAKAI RUNDUNARTA GIRKAS SU KUMA SUN YAKI SICILY .
S HEKARA 1944 WATAN YULI HITILA YAYI ZAMA DA JIGA JIGAN HUKUMARSA DAN GANEDA YAKIN DA SUKEYI KO DAYA SUNKUYA DOMIN YA DUBA TASWIRA SAI WANI BOMB YA FASHE WANDA MUTUN HUDU SUKA RASU SHE KUMA TA SAMI RAUNUKA WANNAN HARI MUTANEN HITILANE SUKA SHIRYASHI DOMIN YANA SASU CIKIN HALKAKA
CIKIN SHEKARAR 1945 RANAR 29 GA WATAN AFRIILU HITILA YAYI WASIYYAR KARSHE WACCE YA MUZANTA YAHUDAWA,SANNAN A WATANNE RUNDUNAR HITILA TA MIKA WUYA GA RUNDUNAR BARITANIYA A ITALIYA, SANNAN WASHE GARI WANI SOJA YA DAGA TUTAR SABIYAWA KAN WANI BENE DA BAIDA NISA DAGA GIDAN HITILA BAYAN HAKA DA KADAN SAI MUTANENSA SUKA JI WANI SAUTI YAFITO DA KARFI DAGA BAKINS ALAMAT YA HADIYE RANSA YA FADI MATTACE ,
ITA KUWA MATARSA SABODA BAKIN CIKI TA SHA GUBA TA BISHI ,
BAYAN HAKANE JAMUS SUKA MIKA WUYA MATAKI MATAKI,A ITALIYA AWATAN MAYU,DAGA NANNE KASASHEN TURAI SUKA KU BUTA DAGA HATSARIN HITILA AMMA SUNYI ASARAR RAYUKA DA DUKIYA WANDA BAZU KIDAYU CIKIN SAUKIBA.
NAKU
AUWAL MUHAMMAD ABDUL KADEER
DAN NAJERIYA A BIRNIN OMDURMAN SUDAN

30.9.07

JAN FURE

15.9.07

KA JI KADAN KA JI MAI YAWA


Ka san me ya faru?

Cikin watan da ya gabata a khartoum babban birnin jamhuriyar sudan, ina tafiya a hankali saboda rashin lafiyar da nake ciki zani asibiti, ban muzgunawa kowa ba kuma ba wanda ya muzguna mun face wannan zazzabin daya fallashi lafiyata a bainar jama'a, ina tafe ina dan sake sake ba wani takamamman tunani da nakeyi duka dai kame kame ne , an jima inyi wakar dankwairo an jima can inyi karanta wata aya, ni kuwa kaftani nasa ba jallabiya ba ba kuma hula kaina, hankalin suma ta ya tashi, ban tsammanin za'a rasa gashin bargo da suka kulla abota da gashina wanda da a kasar hausa ne da yara sun min wasan '"ga wani a bu a kan matan sarki" . ban karkare tone tonen tunani na ba sai sai naji tsawa a baya na

" kai ne limamin wancan masallacin ?"

sai na farka a firgice sai naga wani mutum a yankwane, kasusuwa sun baiyana a fuskarsa , gajere , idanunsa sun yi jajazur kamar gauta , gashi ya daka mun harara.

" a'a ni ba liman bane " nace

" to kai me ye? " ya ja gurnani kamar zakin da aka tsokana

sai naga abun sai hauhawa yake , ga shi sai kokarin huruwa yake

" ni dalibin jami'a ne " nace masa

sai ya zaburo kai na yana nuna mun kashedi yana cewa " wai shin ku 'yan najeriyan nan kafun kozo sudan ba musulunci ne ko yaya? kawai kuna zuwa kuna mana cokiburutsu irin na usama ben laden "

na shafa ko zan ji hakurina , ashe ya sace mun , don haka nima na haukace na fara maganganu da ba nutsuwa ciki " ina ruwanka da 'yan najeriya " " me suka ci maka basu biya ba " " me osama ben laden ya maka " .


Kafin in kare zaiyano abunda ke kwakwalwata sai kawai naga ya suri hoge mai girma wai zai mun rotse
sai nai shiru ina kada kai , na laluba kamus din kaina ban sami komai ba sai wasu kalmomi sai nai maza na hadasu nace " ZA-KA-MUTU! "
Ko da yaji haka sai yace " ka kashe ni a kasa ta? , wannan kasar muce mu mukai gwagwarmaya akan ta "
ba shakka ya fesa mun tsoro a zuciya ta, kuma yasa nayi bitar jimlar da na hada , na karanci ma'anar ta a take sai na fahimci cewa ma'anar ta shine in kashe mutum a garinsu " sai nayi wasu yan sunbatu ina ja da baya da yan dabaru , har na samu na gota shi kuma ya haye katangar hubbaren wani shehunsu mai suna HAMDANNIEL kamar kadangare da dutsen a hanunsa, ni kuwa na wuce ina yiwa kaina barka a raina , don kuwa da ba don kariyar Allah ba da ya kara mun kwankwatsar kayi kan zazzabin nan.

To amma abun tambaya shine me yasa wannan mutumi ya shiga rayuwata na 'yan wadannan dakikai?

AMSA shi dai wannan bakauyen yayi tsammanin cewa najeriya duk kiristoci ne saboda yaga shugabanta Obasanjo kiristane kuma dimukoradiya ta kawo shi , sannan galibin yan kwallon najeriya yaga ba sunan musulmai gare su ba, har sun yi tsammanin Jay Jay okocha musulmi ne mune bamu iya fadan yadda sunan yake a larabci ba wato UKASHA, to duk da haka sai yaje yin salla wami masallaci sai ya tarar limamin dalibine dan Najeriya , don haka yake ganin bai dace ace wadanda suka musulunta jiya da daddare sunzo suna limancin wadanda suka gaji musulunci kaka da kakanu ba.

Amma kai meye ra'yinka

sai naji daga gareka

25.8.07

KWADON DABI'AR DAN ADAM DA MABUDINTA

ABUL HASAN ANNADAWY


Auwal Muhammad Abdulkadir
aazarema@yahoo.com
25-8-07m / 11-8-1228
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata masa ba irin sauran masu gyaran da ke zuwa gidaje ta baya ko su sadado ta taga bane , masu yaki da wasu cututtukan zamantakewa da aibubbukan halaye kawai ba , sai ka samu daga cikinsu akwai masu sa’ar gusar da wasu a sassan wasu garuruwa na dan wani lokaci, wani ma ya mutu bai cimma burinsa ba.
To amma shi manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata yazo wa gidan gyara ta kofarsa , kuma ya sanya wa kwadon dabi’ar dan’adam mabudinta , wannan kwadon yana dawuyar sha’ani saboda bude shi ya gagari masu sauyi kafun manzanci dama duk wanda yai kokarin bude shi bayan shi ba tare da mabudinsa ba.
Ya kira jama’a zuwa ga imani da Allah shi kadai, da kin gumaka da bauta da kafircewa dagutu, don haka ya mike cikin jama’a yana cewa “ ya ku mutane ! Kuce ba abun bautawa da gaskiya sai Allah ku rabauta ( ku sami rabo) ‘’ ya kuma kira su zuwa ga imani da manzanci
da imani da lahira .
Mahatma ghandi na kasar hindu a rayuwarsa ta siyasa da gwagwarma ya takaita jagorancinsa da gwagwarmayar sa kan ka’idoji biyu ne .
Na farko: wanda shine takensa (ba muzgunawa ba kare kai) yayi kira zuwa ga wannan ka’ida a matsayin addini da falsafa cikin hudubobinsa da makalunsa da kuma jaridunsa. Ya karar da karfinsa kan haka , to da yake hanyar daya dauka ba hanya ce mai zurfi wajen sauyin zuciya ba bata yi wani tasirin azo agani wa mutanen hindu ba , don haka suka hure ta , suka kashe rabin miliyan na musulmi a East Punjab da Delhi a 1947 miladiya, daga karshe shi ghandin aka masa kisan gilla dukda daukaka shi da bauta masa da wasu suke yi.
Na biyu: shine shafe matsalar fifiko tsakanin kabila da kabila , wanda baiyi nasarar kirki ba, wannan yankakken dalili ne cewa manhajin annabawa shine ya mafi kyau wajen gyara da sauyi.
fassara daga littafin (( Rashin da duniya tayi samakon faduwar musulmai)) na malam Hasan Annadawi.

18.8.07

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRACI

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRAICI
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR

6/8/1428h-19/8/07m

BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM
Sanannen abune cewa kasashe masu kaffa-kaffa da
addinin su da al'adunsu na kwarai suna kokarin maida
finafinai da wasan kwaikwayo wata kafa ta tattauna matsalar
alumma da tarbiya da bada tunani na gari, sabanin halinda
muke a kasar hausa na karkatar da wannan dama zuwa
gwada kwarewa wajen nuna rashin kunya da da koyawa
manyan gobe munanan dabi'u daga baya kuma sai ace ana
kokarin gyara tarbiya to lallai bamu ba tarbiya har duniya ta
tashi indai yan daba da mata masu cin gashin kansu da
wadanda aka kasa tarbiyarsu suka gudu suka bar tarbiya su
-ne masu tarbiya kai abun dariya da takaici duk da haka
shuwagabanni da wadanda abun ya shafa basu yi yunkurin
hanawa ko kokarin garkatar da akalar fina-finan izuwa koyar
da tarbiyar gaskiya ba . to yanzu abun yakai ga dole kowa ya
ciza yatsa , akwai matukar da takaici ace yar fim ta fito tsirara
har na tsawon dakikai takwas kan gado sannan wani yazo ya
haukanta yayi tsiyar da zaiyi da ita, sannan yayi wani irin
nau'i na wasa da maniyinsa kan cinyarta , kai ! wallahi ,
na'uzu billahi minashshaidanirrajim! wani irin dabbanci kenan?
kuma abun mamaki harda cewa '' a gafarcemu'' amma
wannan yarinya taci sunanta ''HIYANA'' don kuwa ta ha'inci
duk musulmin duniya, ta kuma tona asirin musulmin najeriya.
Duk wani mai zurfin tunani yasan hakan zata faru tunda
kokari suke su kwaikwayi [nigerian film] su kuwa wannan ba
bako bane gunsu, ga wani abunda na taba karantawa jaridar
gaskiya tafi kwabo ''GTK: To, a matsayinki na wadda take fitowa a fina-finan
Hausa da na Turanci, yaya za ki kwatanta bambancin da ke
tsakanin fina-finanmu na Arewa da kuma na Kudanci?
HAUWA MAINA: Ai dai wannan ne ko kuma aka tambaya, za
ku iya fadin bambancin (dariya).
GTK: Amma da yake ke kina cikin harkar ne, ina ganin ke ya
fi cancanta ki yi mana bayani.

HAUWA MAINA: To shi kenan, a gaskiya, ’yan Kudu sun yi
mana fintinkau in dai za a yi maganar gaskiya ce. Amma
Alhamdulillahi mu ma mun fara shiga sahunsu, saboda idan
aka yi la’akari da irin na’urorin da suke amfani da su, to,
yanzu mu ma mun fara samun irin wa]dannan na’urorin. Haka
kuma ’yan wasanmu na Hausa su ma yanzu sun zaburo, suna
kuma kokari sosai. Saboda haka nan ba da jimawa ba za mu
rika hada kafada da kafada da su.''

Hakika abun daya ban mamaki cikin wannan al'amari babu
kamar wasu masu kokarin wanketa da cewa ai ba fim din
tsiraici bane, saboda wannan wani abu ne tsakaninta da
saurayinta bai da alaka da fim, to amma ai ita jaruma ce a
wannan harka ta tarbiya, wa ya sani ko ta sadaukar da kanta
ne wajen gyara al'adun banza har ta fara yada tarbiya kyauta
ana yada ta a blue tooth cikin kayan mutunci , domin ayi koyi
da ita, sannan an sakar muku haka ne , shin wannan baya
gwada cewa wata ran za'a yi hakan a tsare da furodusa da
dukkan shikashikai da sharuddan fim.

sannan wasu kuma sun bige da cewa taci mutuncin hausa-
fulani ina ruwan wannan matsala da hausa fulani , wasu na
cewa daman ba hausawa bane masu yi , hakika wannan
karya ce mai girma da neman wanke kai na banza da wofi ,
to kai in ma haka ne , waya basu izinin shigowa kano, jama'a
kar mu rudi kammu, hausa fulani dai a duniya zamu bar shi
ba wani abu mai anfani gun Allah sai musulunci.

IYAYE : sune kashin bayan tarbiyar 'ya'ya kuma sune
matakin da idan yaro ya rasa ko sukai sakaci dashi rayuwarsa
zata shiga wani yanayi wanda bara aji dadin karshenta ba,
wani yana cewa '' uwa makaranta ce idan ka shirya ta kamar
ka shirya al'umma ne'' kuma kamar yadda kowa ya sani
wadannan masu cin abinci da lalata tarbiyar manyan gobe
galibinsu in bamu ce duka ba sun fuskanci matsala da iyaye
kamar auren dole ko rashin mai riko mai kyau ko rashin tsawa
da kwaba don haka dole iyaye su dau hakurin daukan kaso
mai girma na laifi saboda kaso mai girman ba suke dashi
wajen jibintan yayansu da kuma damar tarbiya.

YAN WASA: saboda sune masu fuskantar da wannan
matsala zuwa ga alumma kai tsaye don haka duk da barrantar
da kan- su da wasu uzurori da suke bayarwa wanda zai yi
wuya su kansu su yarda da su a cikin zukatansu balle
al'umma gaba daya. Su dai kokarin su dole sai sun kwaikwayi turawa alhali kuwa
kowa yana kokarin bada gudumawane daidai al'ummarsa,
idan bature da baturiya sukai wani rashin kunya a wasan
kwaikwayo to saiku duba cewa to shin kowa a cikin jama'arku
ba rike ya ke da addini ba ? ba tare yake da mafadi ba? Shin
burgewa a garemu shine mu fita daga shingen iyaye da
sunan yanci? Wadannan banbance-banbance na addini da
al'ada idan ba'a duba su ba to zamu jima cikin wannan rami,
mu fito mun yi kura duk wanda ya kallemu ba zai iya
maimaitawa ba.

SHUGABANNI: wato duk Wanda yake da damar fada aji
amma bai hango matsalar da zata iya jawowa masu
zuwa ba, ko ya hango baiyi kokarin kawo sauyi ba .

Daga karshe ina kara rokon wanda abun ya shafa da suyi
hattara wajen daidaita wannan wasa inda zaiyi daidai da
addinin jama'arsu da al'adunsu na kwarai , inba haka ba muyi batan bakatantan bamu ga namu bamu ga nasu .

Allah ya raba mu da sharrin shaidan.

11.8.07

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR
aazarema@yahoo.com
Da yawa mun rudu da sanimmu ko bada sanimmu ba kan abunda amurka da yammacin duniya ke farfaganda kai, na yanci, hakkin bil'adama ,sakulanci (secularism), yakan wariya , girmama addinindan adam ko da ya yake, da sauransu . muna kuma ganin cewa wannan wani cigaba ne sakamakon kokarinsu na amfanar da halittu wanda ba'a sansu ba a baya , wanda kuwa duk wadannan addinin musulunci ya baiyana na kwaransu sannan yayi kafar angulu da wofi daga ciki da isassun dalilai na nassi (kurani da hadisi) ko na hankali .
Alkurani ya tabbatar mana cewa manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] rahama ne ga dukkanin halittu , sannan musulunci shine ya sauya alummar larabawa da ke cikin mummunan yanayi na zamantakewa da siyasa da dukkan sassan rayuwa, ibnu abbas yana cewa: “idan kana so kaga yanda jahilcin larabawa ya kai sai ka karanta fadin Allah madaukakin sarki: “ Lalle ne wadanda suka kashe diyansu , saboda wauta bada ilimi ba sunyi hasara ! kuma suka haramta abinda Allah ya azurtasu bisa kirkira karya ga Allah lalle ne sun bace basu kasance shiryaiyu ba ” .[6:140].
Bayani kan sauyin da musulunci ya kawo ba boyaiye bane saidai abunda ya shige mana duhu musulmanmu da kafiranmu shine shin musulunci yazo da abubuwanda yammaci ke takama dasu koko? Kamar yadda muka yi bayani a baya ya tabbatar da wasu, ya kuma sa wasu a gefe.
Zamu iya ganin yadda musulunci ya kimata dan adam cikin fadin Allah madaukakin sarki: “ kuma lalle mun girmama 'yan adam , kuma muka dauke su a cikin kasa da teku , kuma muka azurtasu daga abubuwa masu dadi , kuma muka fifitasu a kan da yawa daga wadanda muka halitta, fifitawa ” [ 17 :70] .
Manzon Allah [tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] da aka tambayeshi hakkin mace gun mijinta sai yace “ ka ciyar da ita idan kaci , kuma ka tufatar da ita idan ka tufata , kuma kar ka bugeta a fuska , kada kuma ci mutuncinta , kar kuma ka kaurace mata saidai a cikin gida” wannan hadisi an samo shi ne kafin wani abu da ake cewa (CEDAW) . Musulunci har wayau ya tabbatar da kulawa da tausayawa yara kamar yadda yazo cikin hadisi cewa wani bakauye yaga manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] ya sunbanci yaro sai yayi mamaki yace shi yana da yara goma amma bai taba sunbantar ko daya ba , sai abun yayi nauyi wa manzon Allah tsira da aminci sutabbata a gareshi har yace: “ to ya zanyi idan Allah ya zare rahama a zuciyarku¡?”.
Musulunci bai ba wariya kafar shiga ba Allah yana cewa “yaku mutane lalle ne mun halittaku daga na miji da mace , kuma muka sanyaku dangogi da kabiloli domin kusan juna”.[49:13]. Kuma cikin hadisi Abu zarri Allah ya yarda shi ya bada labari cewa ya samu sabani da wani danuwansa wanda mahaifiyarsa ba'ajamiya ce ( ba balarabiya ba) sai ya aibace shi da mahaifiyarsa , da labari ya isa wa annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi sai yace: ya kai abu zarri, lallai akwai jahiliya a tare da kai, su 'yan'uwanku ne Allah ya sanya su a cikin hannun ku , don haka ku ciyar dasu daga abunda kuke ci ,kuma ku tufatar dasu daga abunda kuke tufata dashi , kuma kar ku daura musu nauyin da baza su iyaba, idan kuma kun daura musu to ku taimake su,” kamar yadda Allah ya nuna cewa tsoronsa kawai shine fifiko tsakanin jama'a kan wasu sabanin yahudawa masu riya cewa sune zababbun agun Allah [ God’s favoured nation] , kuma sune masu gudanar da tsarin mulkinsu kan tatsuniyoyin da suke samowa daga Attaurar da hannu yayi wasa ciki , kenan su basa raba addini da siyasa amma duk da haka tana samun kariya daga amurka da sauran manyan kasashe , kai har shi kansa BUSH ya kasa aiki da tsarin “ na sarki na fada , na Allah na masallaci” ko “[ Give unto God’s , what a God’s, and unto Caesar what a Caesar;s] tun da an tambayeshi wanene babban malamin falsafa a siyasar sa sai ya kada baki yace : yesu almasihu”. Girmama addinnai kuwa ma'anarsa a musulunci ba shine jin cewa wani addini koma bayan musulunci shine gaskiya ba , innama ma'anarsa zama da kafirai ba tare da tsangwama ba idan an yi alkawarin lumana dasu , Annabi kuwa yayi zaman alkawarida da yahudawa a madina dukda cewa daidaikunsu suna kokarin kashe shi kamar yadda wata bayahudiya ta sa masa guba cikin abinci , kuma sunyi kokarin jefo masa dutsen markade daga kan bene , amma duk da haka bai far musu ba saida suka saba alkawari a fili da suka hada kai da mutanen makkah wajen yakarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. Wannan shine yasha banban da abunda masu kirayen-kirayen sukeyi na tuhuma addini daya cikin dubban addinan duniya da taaddanci , ko jifa da littafin addini daya cikin kazanta , ko siffanta manzon wani addini daya da harijanci da ta'addanci, duk wannan suna yine domin kara kwanakin daularsu , amma kuwa akasin haka ne ke faruwa don kuwa duk sanda suka kunna wata wuta kan musulunci sai samarukansu sun bi diddigi sun fahimci karyansu kuma sakamakon haka su shiga musulunci jama'a- jama'a , Allah ta'alah yana cewa :[ lalle ne wadanda suka kafirta suna ciyarda dukiyoyinsu, domin su tare hanyar Allah , to zasu ciyar da ita ,sa'annan ta kasance nadama a kansu , sa’annan kuma a rinjayesu”, [8:36], kuma yana cewa “ lalle ne , wadanda suka zo da karya wadansu jama'a ne daga cikinku , kada kuyi tsammanin hakan sharri ne a gare ku, a'a alheri ne a gare ku”. [24:11].

Reality

There are many wide spread ideas among westernersprophet Muhammad peace be upon to him , Qoran and islam in general.
Accoding to conservertives ''prophet Muhammad's life is bloody , his teaching is vicious ,and he is founder of the world most intolerancAe religion (islam).
such kind of un objective accusation awake there peaple for searching truth and reality about prophet Muhammad not from his enemy but from what has been sent down to him , and his wisdom .