11.8.07

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA

SHURE SHURE BAYA HANA MUTUWA
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR
aazarema@yahoo.com
Da yawa mun rudu da sanimmu ko bada sanimmu ba kan abunda amurka da yammacin duniya ke farfaganda kai, na yanci, hakkin bil'adama ,sakulanci (secularism), yakan wariya , girmama addinindan adam ko da ya yake, da sauransu . muna kuma ganin cewa wannan wani cigaba ne sakamakon kokarinsu na amfanar da halittu wanda ba'a sansu ba a baya , wanda kuwa duk wadannan addinin musulunci ya baiyana na kwaransu sannan yayi kafar angulu da wofi daga ciki da isassun dalilai na nassi (kurani da hadisi) ko na hankali .
Alkurani ya tabbatar mana cewa manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] rahama ne ga dukkanin halittu , sannan musulunci shine ya sauya alummar larabawa da ke cikin mummunan yanayi na zamantakewa da siyasa da dukkan sassan rayuwa, ibnu abbas yana cewa: “idan kana so kaga yanda jahilcin larabawa ya kai sai ka karanta fadin Allah madaukakin sarki: “ Lalle ne wadanda suka kashe diyansu , saboda wauta bada ilimi ba sunyi hasara ! kuma suka haramta abinda Allah ya azurtasu bisa kirkira karya ga Allah lalle ne sun bace basu kasance shiryaiyu ba ” .[6:140].
Bayani kan sauyin da musulunci ya kawo ba boyaiye bane saidai abunda ya shige mana duhu musulmanmu da kafiranmu shine shin musulunci yazo da abubuwanda yammaci ke takama dasu koko? Kamar yadda muka yi bayani a baya ya tabbatar da wasu, ya kuma sa wasu a gefe.
Zamu iya ganin yadda musulunci ya kimata dan adam cikin fadin Allah madaukakin sarki: “ kuma lalle mun girmama 'yan adam , kuma muka dauke su a cikin kasa da teku , kuma muka azurtasu daga abubuwa masu dadi , kuma muka fifitasu a kan da yawa daga wadanda muka halitta, fifitawa ” [ 17 :70] .
Manzon Allah [tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] da aka tambayeshi hakkin mace gun mijinta sai yace “ ka ciyar da ita idan kaci , kuma ka tufatar da ita idan ka tufata , kuma kar ka bugeta a fuska , kada kuma ci mutuncinta , kar kuma ka kaurace mata saidai a cikin gida” wannan hadisi an samo shi ne kafin wani abu da ake cewa (CEDAW) . Musulunci har wayau ya tabbatar da kulawa da tausayawa yara kamar yadda yazo cikin hadisi cewa wani bakauye yaga manzon Allah[tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi] ya sunbanci yaro sai yayi mamaki yace shi yana da yara goma amma bai taba sunbantar ko daya ba , sai abun yayi nauyi wa manzon Allah tsira da aminci sutabbata a gareshi har yace: “ to ya zanyi idan Allah ya zare rahama a zuciyarku¡?”.
Musulunci bai ba wariya kafar shiga ba Allah yana cewa “yaku mutane lalle ne mun halittaku daga na miji da mace , kuma muka sanyaku dangogi da kabiloli domin kusan juna”.[49:13]. Kuma cikin hadisi Abu zarri Allah ya yarda shi ya bada labari cewa ya samu sabani da wani danuwansa wanda mahaifiyarsa ba'ajamiya ce ( ba balarabiya ba) sai ya aibace shi da mahaifiyarsa , da labari ya isa wa annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi sai yace: ya kai abu zarri, lallai akwai jahiliya a tare da kai, su 'yan'uwanku ne Allah ya sanya su a cikin hannun ku , don haka ku ciyar dasu daga abunda kuke ci ,kuma ku tufatar dasu daga abunda kuke tufata dashi , kuma kar ku daura musu nauyin da baza su iyaba, idan kuma kun daura musu to ku taimake su,” kamar yadda Allah ya nuna cewa tsoronsa kawai shine fifiko tsakanin jama'a kan wasu sabanin yahudawa masu riya cewa sune zababbun agun Allah [ God’s favoured nation] , kuma sune masu gudanar da tsarin mulkinsu kan tatsuniyoyin da suke samowa daga Attaurar da hannu yayi wasa ciki , kenan su basa raba addini da siyasa amma duk da haka tana samun kariya daga amurka da sauran manyan kasashe , kai har shi kansa BUSH ya kasa aiki da tsarin “ na sarki na fada , na Allah na masallaci” ko “[ Give unto God’s , what a God’s, and unto Caesar what a Caesar;s] tun da an tambayeshi wanene babban malamin falsafa a siyasar sa sai ya kada baki yace : yesu almasihu”. Girmama addinnai kuwa ma'anarsa a musulunci ba shine jin cewa wani addini koma bayan musulunci shine gaskiya ba , innama ma'anarsa zama da kafirai ba tare da tsangwama ba idan an yi alkawarin lumana dasu , Annabi kuwa yayi zaman alkawarida da yahudawa a madina dukda cewa daidaikunsu suna kokarin kashe shi kamar yadda wata bayahudiya ta sa masa guba cikin abinci , kuma sunyi kokarin jefo masa dutsen markade daga kan bene , amma duk da haka bai far musu ba saida suka saba alkawari a fili da suka hada kai da mutanen makkah wajen yakarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi. Wannan shine yasha banban da abunda masu kirayen-kirayen sukeyi na tuhuma addini daya cikin dubban addinan duniya da taaddanci , ko jifa da littafin addini daya cikin kazanta , ko siffanta manzon wani addini daya da harijanci da ta'addanci, duk wannan suna yine domin kara kwanakin daularsu , amma kuwa akasin haka ne ke faruwa don kuwa duk sanda suka kunna wata wuta kan musulunci sai samarukansu sun bi diddigi sun fahimci karyansu kuma sakamakon haka su shiga musulunci jama'a- jama'a , Allah ta'alah yana cewa :[ lalle ne wadanda suka kafirta suna ciyarda dukiyoyinsu, domin su tare hanyar Allah , to zasu ciyar da ita ,sa'annan ta kasance nadama a kansu , sa’annan kuma a rinjayesu”, [8:36], kuma yana cewa “ lalle ne , wadanda suka zo da karya wadansu jama'a ne daga cikinku , kada kuyi tsammanin hakan sharri ne a gare ku, a'a alheri ne a gare ku”. [24:11].

6 comments:

Anonymous said...

Il semble que vous soyez un expert dans ce domaine, vos remarques sont tres interessantes, merci.

- Daniel

Anonymous said...

I'm extremely impressed with your writing skills and also with the format in your blog. Is this a paid theme or did you customize it your self? Either way keep up the nice high quality writing, it's
rare to see a nice blog like this one these days..

my blog ... landhausmode chemnitz

Anonymous said...

Asking questions are truly fastidious thing if you are not understanding anything fully, however this
piece of writing provides fastidious understanding even.


my website: trachtenmode riehl

Anonymous said...

Hi it's me, I am also visiting this web page regularly, this site is truly nice and the users are truly sharing nice thoughts.

my weblog buy twitter followers cheap

Anonymous said...

Hello! Someone in my Facebook group shared this website with
us so I came to take a look. I'm definitely enjoying the information. I'm bookmarking and will be
tweeting this to my followers! Exceptional blog and outstanding design and
style.

my web page: tipps zum abnehmen gratis

Anonymous said...

Hello would you mind sharing which blog platform you're using? I'm looking
to start my own blog in the near future but I'm having a tough time selecting between BlogEngine/Wordpress/B2evolution and Drupal. The reason I ask is because your layout seems different then most blogs and I'm looking for something unique.
P.S My apologies for getting off-topic but I had to ask!


my weblog - halong bay airport