4.6.08

Malam Isa da Alhaji Mu'azu



Ba shakka tunda aka fito da wannan sabuwar siyasa ko ince tun 1999 Malam isa yuguda ne yayi gwamna a jihar Bauci da zabe mai tsarki , don kuwa zaben farko tsakani PDP da APP ba Ahmad Mu'azu ne ya lashe ba , baba Ajiya ne yayi kaye ( kan wuka mai wuyan kamu) amma tsagera suka masa rashin kunya , sannan lokacin ta zarce ma baici ba saboda kowa na bukatar masara ida a rufe don haka masara sak ! ake yi . Amma da tura ta kai bango lokacinda jama'a suka fahimci cewa wannan mu'azun dan rainin wayo ne , suka fito kwansu da kwarkwatansu don su hana shi sanata su hana dan gaban goshinsa Nadada umar gwamna , suka sadaukar da kansu suka don kwato yancinsu daga mahandama , suka tabbadar hikimar Hausawa mai cewa " Sarkin yawa yafi sarkin karfi " .
sau da dama yayin da za'a zalunci mutanen bauci , da sunyi wani dan kokarin kwato hakkinsu sai wani mai anguwa ko yaje gidan rediyo yace wai an san Bauci da zaman lafiya , tun sanda Shehu usumanu ya musu addu'a " . ko me yasa jama'ar Bauci suka yasar da irin wadannan sakarkaru maganganu? , ina ganin wuce irin azaba suka sha a zamanin Amadu mu'azu.
A zamanin Amadu a tunanina babu wani abun da yayi wanda ya ja hankalina kuma na jinjina masa kamar kokarin da yayi na taimakawa musulman pilato , fara daga rigimar addini na 11 ga watan satumban 2001 har izuwa rikicin yalwan shendam , ba shakka wannan abun azo a gani ne.

Wani abunda kuma zamu iya fahimta harwayau shine duk irin badakalar da aka shirya a zamanin PDP a jihar Bauci yuguda yana da kaso a ciki ,yayi shekara takwas cikin jam'iyar hasalima za'a iya fahimtar cewa gogaiya suke da Amadu mu'azu kan jagorancin jihar , don koda sabanin da ke tsakaninsu ya baiyana a sarari har gamagarin jam'iya suka fahimta sai ya baiyana cewa daman don Isa yuguda suke jam'iyar ba don mu'azu ba , wannan kuwa baya rasa nasaba da irin sake hanu da facaka da ya kware kai, sannan ba wanda ya isa ya wanke Isa dangane da irin murdiyar zaben 2003 wanda shi yaki a masa 2007 ,
ah ashe ba dadi ?!

wata tsaka mai muya da malam Isa ke fuskanta ita ce matsalar 'Yan -sara -suka duk da cewa sun dasu kuma suka ciro a mukumar Alhaji mu'azu to amma a hukumar malam Isa sun riga , sara da sassaka baya hana su toho .

Amma ko ba komi kamar yadda malam Abubakar gero ke cewa " Da bakikkirin gwara baki-baki "

Naku Alkalami.

3 comments:

Anonymous said...

Genial post and this fill someone in on helped me alot in my college assignement. Thank you for your information.

Anonymous said...

hi!,I like your writing very much! share we keep in touch
extra approximately your post on AOL? I
require an expert on this house to unravel my problem.
Maybe that is you! Looking forward to peer you.


Here is my web-site - landhausmode größe 52

Anonymous said...

I'm impressed, I must say. Rarely do I come across a blog that's both equally educative and amusing, and let me tell you,
you've hit the nail on the head. The problem is something which too few people are speaking intelligently about. I'm very
happy I stumbled across this in my search for something relating to this.


Feel free to surf to my web-site ... halong bay accident