9.8.08

Rayuwar da Alkalami bazai manta ba


Ya salam ! , komi yai farko zaiyi karshe , shekara kuma kwana ne , kamar kwana hudu da suka gabata na sauka a filin jirgin Khartoum da Abokan karatuna kamar karfe 9:00 pm , lokacinda aka fito damu zuwa masaukinmu ba abunda nake kokari sai in kalli yanayin farkon kasar da na fara shiga ba tare da na kyafta ido ba , musamman sanda muka hau gadar da ke kan Nilu in da na hangi wani dan karamin tsibiri a ciki , haka dai cikin kallace-kallacen gari da masu garin , muka isa masaukinmu , wasu fuskokinda dama munsansu suka taryemu da sowa , wadanda suka fara ganinmu a ranar kuma suka mana barka da zuwa kowa yaje kashe wutar gabansa .
Ni dai fatata da tsikar jikina tana isar mun da sakon bakunta , da kewar gida Najeriya .

Wani gari da waye , dan uwa Bashir ya tattaremu muka je wani abu mai kamada rangadi a Jami’ar musulunci ta Omdurman (Omdurman Islamic University ) wacca itace aka bamu gurbin karatu a ciki , dama dai ina da karamin sani dan gane da Jami’ar , saboda kanen kakana Ambasada Abba Abdulkadir samada shekara 30 shima nan yayi karatu , wata ran kuwa da akayi sharan dakin littafansa , an bani wasu littafansa daga ciki harda Dalilin( brochure) tsangayar osuluddin , a matsayina na dalibin Arabiya .

Mun fara karatun A jamiar inda na shiga tsangayar shari’a and law , muna tattaki wani lokacin yayi saibi kamar tafiyar hawainiya wani kuwa muga kyaftawa da bisimillah ya gilma kamar walkiya , wata rayuwar tai mini zaki kamar zuma wata tai mun daci kamar shuwaka , wata kuwa tamun tsami kamar tsamiya , tsada ko lemon tsami .
Mun shiga fargaba daban daban kamar mutuwan mataimakin shugaban kasa kuma tsohon dan tawaye daya fadi a jirgi bayan kwana Ashirin da bashi mataimakin shugaban kasa , cikin birnin Khartoum ya dauki dumi don kuwa wasu sun rasa rayukansu wasu sun rasa dukiyoyinsu wasu matan kuwa sun rasa mutuncinsu sakamakon fyade da mutanen mamacin sukayi da hujjar cewa hukuma ce tai kutunguilar kashe shi , ni dai ban rasa komi ba sai aminci da tsoro ya koreshi , sai kuma hawaye saboda wata motar kabokabo da aka kona a kofar gidanmu , hayakinta ya ringa tultula gidanmu .

Abunda yafi tada hankalina babu kamar rashin lafiya da nayi a karshen shekara ta uku wata biyu ana mun allura ina kuma hadiyar kwayoyi takwas, sauran wata shida kuma ina shan kwayoyi bibiyu duk wayewar gari . wannan mawuyacin yanayi da jikina ya shiga ya kama hanun zuciyata sun tafi don kuwa har nayi shawarar jingine karatun zuwa shekara mai zuwa in dawo gida don jinya ,
Cikin wannan rashin lafiyar kuwa Allah ya jarrabeni da yan sudan don kuwa farko-farkon ciwon wataran na kama hanya zuwa asibiti ina tattaki ina karatu wani sa’in ina wata yar waka da zata sanyaya mun zuciya ita kuma ta sanyaya mun jikina , ni kuwa kaftani nasa ba jallabiya ba, ba kuma hula kaina, hankalin suma ta ya tashi, ban tsammanin za'a rasa gashin bargo da suka kulla abota da gashina wanda da a kasar hausa ne da yara sun min wasan '"ga wani a bu a kan matan sarki" . ban karkare tone tonen tunani na ba sai sai naji tsawa a baya na

" kai ne limamin wancan masallacin ?"

sai na farga a firgice naga wani mutum a yankwane, kasusuwa sun baiyana a fuskarsa , gajere , idanunsa sun yi jajazur kamar gauta , gashi ya daka mun harara. Ya kuma nuna wani masallaci , wanda ni banda wata alakata dashi data wuce cewa wani lokaci na kanzo karatu ciki ba , anan ne kuwa na taba ganin tsohon shuguba Sadiq al-Mahdi yazo daurin aure .

" a'a ni ba liman bane " nace

" to kai me ye? " ya ja gurrnani kamar zakin da aka tsokana

sai naga abun sai hauhawa yake , ga shi sai kokarin huruwa yake

" ni dalibin jami'a ne " nace masa

sai ya zaburo kai na yana nuna mun kashedi yana cewa " wai shin ku 'yan najeriyan nan kafun kozo sudan ba musulunci ne ko yaya?

na shafa ko zan ji hakurina , ashe ya sace mun , don haka nima na haukace na fara maganganu da ba nutsuwa ciki " ina ruwanka da 'yan najeriya " " me suka ci maka basu biya ba " .


Kafin in kare zaiyano abunda ke kwakwalwata sai kawai naga ya suri hoge mai girma wai zai mun rotse
sai nai shiru ina kada kai , na laluba kamus din kaina ban sami komai ba sai wasu kalmomi sai nai maza na hadasu nace " ZA-KA-MUTU! "
Ko da yaji haka sai yace " ka kashe ni a kasa ta? , wannan kasar muce mu mukai gwagwarmaya akan ta "
ba shakka ya fesa mun tsoro a zuciya ta, kuma yasa nayi bitar jimlar da na hada , na karanci ma'anar ta a take sai na fahimci cewa ma'anar ta shine in kashe mutum a garinsu " dukda cewa dai dama barazana ce ,sai nayi wasu yan sunbatu ina ja da baya da yan dabaru , har na samu na gota shi kuma ya haye katangar hubbaren wani shehunsu mai suna HAMDANNIEL kamar kadangare da dutsen a hanunsa, ni kuwa na wuce ina yiwa kaina barka a raina , don kuwa da ba don kariyar Allah ba da ya kara mun kwankwatsar kayi kan zazzabin nan.

To amma abun tambaya shine me yasa wannan mutumi ya shiga rayuwata na 'yan wadannan dakikai?

AMSA shi dai wannan bakauyen yayi tsammanin cewa najeriya duk kiristoci ne saboda yaga shugabanta Obasanjo kirista ne kuma dimukoradiya ta kawo shi , sannan galibin yan kwallon najeriya yaga ba sunan musulmai gare su ba, har sun yi tsammanin Jay Jay okocha musulmi ne mune bamu iya fadan yadda sunan yake a larabci ba wato UKASHA, to duk da haka sai yaje yin salla wami masallaci sai ya tarar limamin dalibine dan Najeriya , don haka yake ganin bai dace ace wadanda suka musulunta jiya da daddare sunzo suna limancin wadanda suka gaji musulunci kaka da kakanu ba.

Amma kai meye ra'yinka

sai naji daga gareka
Bayan kwana biyu ko kasa da haka ko sama da haka wani abunda da yafi takaici gareni ya faru , shima na fito zani Asibiti ban san sami mota da wuri ba , sai daga karshe motar da na samu ta cika sai a tsaye na tsaya banyi auni ba sai naji naushi koda na juyo sai kowa yak au da kai , sai kawai wani baba dake bani hakuri , koda na kuma juya wa sai na kuma ji wani naushin sabo , na juyo cikin fushi da radadin rashin lafiya , sai babannan ya kara bani hakuri , duk wadannan naushe-naushe ban san mai yinsu ba kuma ban san daliliba , sai daga karshe naji wai sanda nake tsaye na taka wani dan kudancin garin kuma da alama cikin maye yake , amma abun mamaki koda nayi martani cikin fushi sai na zama mai laifi , mata da maza na mota sukace dama mu baki mune muke kawo rigingimu cikin sudan , muryoyi daban daban wata a baiyane wata a dashe kowa yana mun tofin Alatsine , koda naga abun ya kasa hawa mizanin adalci saina dakatarda Karen mota nace ya sauke ni na kara da addu’a a baiyane kowa a motar saida yaji nace “ Allah ka fitar damu daga garin azzalumai ” .

Wadannan ababa da suka faru dani har suka sani cikin damuwa wani abune dake gwada cewa rayuwa launin fari ne wata ran kuma baki wataran kasha zuma ,wataran kuwa kasha madi , wataran kasha madaci ,don kuwa zaiyi wuya mutum ya sami mutumin kirki a doron kasa kamar dan sudan mai girmama kowa da rashin girman kai , mutane duka daya ne maikudi da talaka , koda kuwa shugaban kasa ne , yana daga abunda muka ji labari daga wadanda suka rigayemu cewa sanda akai wuyar man fetur a kasar shugaban kasa in ya fito yakan debi yan kasa ya rage musu hanya , lokacin muna nan kuwa wataran da sudais ya kawo ziyara kasar jama’a kamar tawagar tururuwai kowa na so ya gaisa dashi , koda shugaba yaga an gajiyar da bakonsa sai ya kutso ya tare shi yaba jama’a baya yana hanasu sai suka ture shugaban kasa yai kasa koda yaga abun yafi karfinsa saiya ja gefe , muma almajirai mukan halarci wasu tarukan da shugaban kasa ke zuwa kuma mu zauna a sahun gaba – gaba , ina tuna wata ran da ya shigo taro aka mike ana taken kasa nidai da Habib tijjani da Ibrahim muktar bamu mike ba kuma tsakaninmu da shugabansa baifi sahu hudu mukai ido hudu dashi amma muka ki mike , kuma muka ki mike wa muma mu sandare , Allah ja zamaninka Bashir .

Cikin wannan tattaki daga yini zuwa yini ,mako zuwa mako , wata zuwa wata , shekara zuwa shekara , muka farka muke jin kamar labarin cewa muna shirin jarrabawar fita a jami’a , wannan ya razana zuciyata matuka , musamman inya tuna cewa ya kamata mutun ya karbi sakamakonsa da hanun dama yaje gida yana kadata kamar tuta kowa ya gani , muna cikin jarrabawa “ wataran ina karatun jarrabawa a wani masallaci mai jan fenti a gefen titi , dama dai munji wani abukamar jitajita cewa yan tawaye zasu shigo da niyar juyin mulki , amma duk mun dauka kamar yadda suka saba ne , suce zasu zo amma ba ganin ko kuransa , da haka nidai na dauko littafin Public finance ina karantawa saboda jarabawansa zamuyi jibi , koda na leko ta taga sai naga gare ya sake fuska kamar ba wanda na sani ba sai na fito in ganewa idona koda muka fito sai naga jerin gwanon motocin masu sulke da na take suka fara bude wuta cikin iska , wani yanayi ne wanda ban taba tsammanin zan sami kaina a ciki , a lokacin na san ma’anar tawaye da kokarin juyin mulki , ana ta rowan harsashai masallaci kuma ya zama kamar kasuwa kowa ya fado ciki , maza da mata , musulmi da aljihun baya, kowa wasu na rarrafe wasu na ni kuma ina bayan ginshikin masallaci tsoron kada a harbo wani abu ya fasa gini ya shigo ya mun rauni , kuma ba shakka hakan ta faru amma Allah ya tsare , sudai wadannan yantawaye sun fara jin kanshin gidan shugaban kasa , amma karshe sunyi kicibis da dakarun hukama inda aka ba hammata iska aka taushe su aka kamasu , sai dai abun takaici cikinsu akwai kananun yara yan shekara12 , 13, 14, wasu an kaisu barzahu wasu an kamesu .

Cikin bugawar zukata muka kare wannan jarrabawa amma da ikon Allah sakamakon ya fito na sami matakin na biyu a tsarin darajar sakamako wato Very good wanda yake farawa daga 70 zuwa 79 ,

Na kare rayuwata ta sudan zan barta ina mai tuna ranarta da tasha banban da irin ranar sauran duniya , wacca Allah ya kwararar da Nilu a cikinta manoma suna kwararawa wa gonakinsu dake bakin gaba , makiyaya suna shayarda dabbobinsu , masunta suna kamun kifi , ni kuwa almajiri a ina shan wata iska mai debo danshi zuwa gare ne , ina jin dadin haddan abun day a wajaba in haddace , ina fahimtar abunda ya wajaba in fahimta , ba shakka rayuwa ce mai dadi amma ban san abunda yafi dadi ba shin sanin wani waishi bashir dab sakkwato , wanda ya dauke ni kaninsa yake ban hakuri don inci abinci kamar karamin yaro , wanda ya gama karatunsa ya tafi ya barni kamar maraya , ko haduwa da Mustapha bangon gishiri dan shehu barnoma , ko Habibu tijani da muka karasa rayuwar da muka fara a Jos ko Ibarahim dan baba wanda na sanshi a nan sudan amma kamar tare mukai yaranta , ko yusuf Nabahani comtuper man , ko Awwal bakoshi bangon dutse mai wuyar isa , ko umar hamza maim un ahnun ka mai sanda daga nesa , ba shakka rayuwace mai zaki kuma wucewarta daci ne dauwamamme .

Bazan iya mance kirkin muttanen dakin da nake kaikawo zuwa gareshi ba , sai sani musa ya miko mun magani na in sha , kabiru a bamu wani labarin raha , Naziru ya fadakar dani zubairu miko mun taliyar Indomie , bana fita daga dakin sai sun warkar da jikina da zuciyata , Allah ya bar zumunci.

10 comments:

dan sudan said...

sallama ga reka dan uwa ina mutukar murna da nakaranta wannan file naka ka yi kokare sosai ina fata allah yataimake ka koma yabaka abin da kake nema amin irin ku masu kishin yaren hausa kadan kukasamu cayauar kujira da gida najeria kuna iya taimakawa hashen hausa ya ci kaba inafata allah yataimakeku amin

dan sudan said...
This comment has been removed by the author.
Anonymous said...

MURNA DAGA KASAR (IMANI)YEMEN da kuma fatan alkhairi ga yanuwan mu dalibai da Allah yayi musu taimakon kammala karatun su.da fatar Allah yayi mana jagoranci a cikin rayuwar mu amin.
Abu-Muhammad
sanaa yemen

Anonymous said...

Tabbas malam auwal kayi kokari yadda ka daure duk irin fadi tashin da kashiga yayin karatun ka. haka akasan namiji da dauriya a kan dukkan lamuransa..ban boye maka ba, kadan ya rage in zubda hawayen don tausayi da naji lokacin karanta wanna dogon kasidar taka, musamman inda kace yan tawaye sunzo yin juyin mulki da inda ka shiga mota aka nusheka. nayi bakin ciki matuka kamar ni akayi ma bin, daya komai mai zuwa da wucewa ne, gashi yau yaza ma labari..Allah yayi mana jagora a dukkan ayyukan mu na yau da kullum.

Anonymous said...

Howdy,

When ever I surf on web I come to this website[url=http://www.weightrapidloss.com/lose-10-pounds-in-2-weeks-quick-weight-loss-tips].[/url]alkalami.blogspot.com really contains lot of useful information. Let me tell you one thing guys, some time we really forget to pay attention towards our health. In plain english I must warn you that, you are not serious about your health. Research points that almost 50% of all USA adults are either chubby or overweight[url=http://www.weightrapidloss.com/lose-10-pounds-in-2-weeks-quick-weight-loss-tips].[/url] Hence if you're one of these citizens, you're not alone. In fact, most of us need to lose a few pounds once in a while to get sexy and perfect six pack abs. Now the question is how you are planning to have quick weight loss? [url=http://www.weightrapidloss.com/lose-10-pounds-in-2-weeks-quick-weight-loss-tips]Quick weight loss[/url] is not like piece of cake. You need to improve some of you daily habbits to achive weight loss in short span of time.

About me: I am blogger of [url=http://www.weightrapidloss.com/lose-10-pounds-in-2-weeks-quick-weight-loss-tips]Quick weight loss tips[/url]. I am also health trainer who can help you lose weight quickly. If you do not want to go under difficult training program than you may also try [url=http://www.weightrapidloss.com/acai-berry-for-quick-weight-loss]Acai Berry[/url] or [url=http://www.weightrapidloss.com/colon-cleanse-for-weight-loss]Colon Cleansing[/url] for effortless weight loss.

Anonymous said...

I read this piece of writing fully on the topic of the resemblance of most
up-to-date and previous technologies, it's amazing article.
My blog post instant cash loans

Anonymous said...

Youг article featureѕ veгіfied beneficial to me ρеrsonally.
It’s quite useful and уou're obviously quite experienced in this field. You get opened my personal face in order to different views on this specific topic together with intriquing, notable and solid content.

Stop by my site :: Buy Valium
Look into my web site ... Buy Valium Online

Anonymous said...

Good article! We will be linking to this great content on our site.
Keep up the good writing.

Here is my weblog :: trachtenmode in mammendorf

Anonymous said...

First of all I want to say superb blog! I had a quick question which I'd like to ask if you don't mind.
I was interested to know how you center yourself and clear your mind before writing.
I have had a hard time clearing my thoughts in getting my ideas out.
I truly do enjoy writing however it just seems like the first
10 to 15 minutes tend to be lost simply just trying to figure out how to begin.
Any recommendations or tips? Kudos!

Here is my web-site - landhausmode ludwigshafen

Anonymous said...

I really like your blog.. very nice colors & theme.
Did you design this website yourself or did
you hire someone to do it for you? Plz respond as I'm looking to create my own blog and would like to know where u got this from. many thanks

my web blog :: tipps zum abnehmen an den beinen