9.8.08

shin zamu iya fahimtar gaskiya tsakanin shi'a da sunna ta waki'oin siyasa ?

Iran da Amurka fuska biyu ga kobo daya

Dalilin wannan tambaya shine wani rubutu da naga wani bawan Allah yayi yana mai tabbatar da ingancin mazhaban shi’a wanda ya ginu kan zagin sahabbai , da matan manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi , da irin gaban dake tsakanin Jamhuriyar Iran , da kasar Amurka , ko artabun da akai tsakanin Hizbullah da Isra’ila .

Sau da dama hakan ake tunani , sai muyi wa mangoro hakunci da bawon da ya lillubeshi , wannan kuwa zai boye mana da dama daga cikin gaskiyar da muke nema , wannan ma ya tunamun wani da yayi shigan wani Akaramakallahu , da babban rawani da duk kayan da jama’a zasu yi tsammanin Shi na kwarai ne , ya sauka wani gida wanda daga karshe ya sace musu yaro yayi gaba .

Ya kamata mu tuna cewa siyasa abace da ke ta’allake da alfanu , kowace kasa ta hangoshi zata garzaya ta kawo wa kanta , ko da daga makiyarta ce , sai tayi mata zakin baki da lallashi , don haka wasu suke ganin siyasa ba makiyi na dindindin ba kuma aboki na dindindin .

Ita dai gaskiya daya ce amma in muka dauki ma’aunin da wannan dan shi’a ke amfani dashi zamu ga gaskiya sun zama barkatai , saboda Amurka bata da abokin gabanda ya wuce Osama ben laden , tunda shine ya kwance mata a kasuwa , ya gwada wa duniya cewa Amurka bata isa tayi aikin Allah Ta’ala ba . kuma har tayi nasarar tabbatar wa Al’umar duniya , majalisar dinkin duniya da daukacin kasashe cewa shi dan ta’adda ne kuma ya wajaba a kawo shi ko gawarsa , alhali kuwa bai taba hada hanya ma da shi’a ba bare ya shiga .

Akwai misalai da dama da zai tabbatar mana da cewa siyasa babu wani hali mai dorewa wanda ba mamaki babbansu ya zama alakar Iran da Amurka ta inda suka raba gari wajen mas’alar makamin kare dangi , sannnan sukayi taraiya wajen kawo tashin hankali , da kawo rudu a kasar Iraki, musamman in muka san cewa Badr corps da jaishul mahdy a iran ake horasu a turosu don zubar da jini da tarwatsa garuruwan Ahlussunnah , duk su gudu don kar ya zama suna da wani matsuguni na musamman , don Shi’a su zama sune mafi yawa .

Yayin da muka so sanin zurfin Alaka tsakanin Amurka da Iran wanda masu sharhin siyasa ke ganin fuska biyu ne ga kobo daya , tana nan tun baiyanar Khomeini a matsayin dan hamaiya ga hukumar Shah . cikin Hirar da akayi da Bani Sadr (shugaban kasa na farko bayan juyin khomeini) a shirin ZIYARA KHASAH a gidan talabijin na Aljazeerah ya tabbatar cewa “ wakilan White House sunzo don ganawa da Khomeini a Neauphle le chateau inda yake gudun hijira , wanda Ibrahim Yazdi ne ya taryosu (wazirin harkokin waje a hukumar Mehdi Bazargan ) , anyi zaman da ya hada da jakadan Amurka a Tehran da Mehdi Bazargan da sauran ayoyi wanda suka dauki matakin hadin guiwa tsakanin malamai da sojoji don a samar da tsarin siyasa tsayaiye a Tehran ”, haka kuwa Khomeini ya bar Paris cikin jirgi mallakar faransa wanda aka ware masa shi da masu dafa masa baya ya sauka filin jirgin Mehrabad na Tehran 1/2/1979 abun mamaki Amurka bata tanka ba .

Zaiyi wuya wani ya gaskata cewa ba hanun Amurka a kifar da mulkin Shah saboda a daidai lokacin da hakan ya faru akwai sojojin Amurka 40,000 dubu arba’in suna aiki ma’aikatar jikin gida da tsaro da SAVAK ( Hukumar liken asiri ta a mulkin Shah ), kuma suna da tare da manyan kayan liken asiri.


Har wayau dangane da kawancen Iran da isra'ila Bani sadr cewa yayi
“ lokacinda mukai zama da sojoji ,wazirin tsaro yai bayanin cewa abun muke shiri shine sayan makamai daga Isra’ila , munyi mamakin hakan , don haka na tambayeshi , waya saka hakan? Yace : Imam Khomeini , nace wannan bazai yiyu ba , yace kasan bazan yi hakan da radin kaina ba , don haka na garzaya don ganawa da Khomeini na tambayeshi , kai ka bada dammar haka ? yace eh musulunci ma ya bada dammar yin hakan , kuma yaki shine yaki, abun ya daure mun kai , ba shakka haka ne amma ni nayi tsammanin yakinmu tsabtatacce ne , kuma jihadi shine mu yardar da yan’uwanmu su dakatar da yaki su fuskanci zaman lafiya , wannan abunda da ya wajaba ba zuwa sayo makami a Isra’ila don yakin larabawa ba, bazan yarda da haka ba , sai yace mun “ kai kana adawa da yaki , kuma dole ka yi don kaine a gurbin jagoranci ” haka babban wazirin Isra’ila Menachem Begin ya tabbatar da cewa suna taimakawa kasar Iran da makamai , shi kuma Ariel Sharon (wazirin tsaro a wancan lokacin) ya baiyana cewa suna hakan ne don raunana Iraki .

Daga cikin abunda ke razana Iran babu kamar wata kasa ta zanto tana makwabtaka da ita kuma jagororinta daliban addini ne wadanda basu bata kwakwalensu da munafunce-munafuncen siyasa ba , don wannan zai hana shigarda shi’anci a duniya , don haka ba wanda yaci moriyar ranar 11/9/2001 kamar Iran , don haka faduwar hukumar Taliban tamkar sakiya ne ga marurunta , kuwa tun tuni tana taimakawa Northern Alliance dake Mazār-e Sharīf , da tsirarun yan shi’ar kasar dake yankin Bāmiān har takai ta fara barazanar kawo sojojinta a iyakarta da Afganistan to kada Amurka kudiri aniyar yakar Taliban sai zamu ta tarda mujemu . don haka Iran ta hanzarta yarda da hukumar Hamid Karzai wanda Amurka ta kafa , shi yasa jakadan Iran a Afghanistan Muhammad Ridha Hashimy yace “ sabanin da ke tsakanin muda Al’ummar duniya tasirinsa bai baiyana a Afghanistan ba har yanzu ,kuma muna ganin lallai Afghanistan zata iya kasancewa sanfuri ga irin taimakekeniya tsakanin Tehran da Al’umar duniya ” kuma kowa zai iya fahimtar ma’anar Alummar duniya anan da cewa Amurka ake nufi , don sune jagoran yaki .

Har wayau Muhammad Abtahy a taron da sukai a Abu Dhabi
“ da badon Iran ba da Kabul da Bagadaza basu fadi ba ” .

Taraiyar Iran da Amurka kan yakar Iraki a 2003
Iran ta yi ruwa tayi tsaki wajen wannan yakin kai tsaye ko sunkuye ta hanyar Da‘wa Party da Supreme Council of the Islamic Revolution in Iraq (SCIRI), shiyasa yake a baiyane Amurka ta hada kai da shi’ar Iraki ta kuma gadar musu da mulkin Iraki su kuma sunci karensu ba babbaka kan yan sunna , suka tilasta musu kaura , sun kashe malaman masu adawa da siyasar Iran a Iraki.

Idan mai rubutu zai yi batun alakar hadin kan Amurka da Iran a Iraki (raunanniya) dole sai ya ambato wasu abubuwa kamar haka :

1- Tehran da Washinton suna da wasu cinikaiya irin tasu a boye duk da cece-kucen da suke a kafafen watsa labarai .

2- Ba kunya ba tsoron Allah Iran tayi kakagida kan al’amuran cikin gida a Iraki , don kuwa galibin masu madafan iko kasar imma yan kasar iran ne ko masu Nationality na Iran , sannan Badr Corps da Supreme Council of the Islamic Revolution in Iraq (SCIRI) suna samun horo ne daga Iran sai a watsosu Iraki don kisan gilla wannan duk Amurka tana sane da hakan , amma saboda cinikaiyarsu bata ce uffan .

Har ila yau rahoton da Robert Gates da Zbigniew Brzezinski sukayi kan Alakar kasashen biyu wanda suka samai taken Iran: Time for a New Approach , rahoton ya baiyana mahimmncin ganawa tsakanin biyu saboda dalilan siyasa da istiratijiya na alfanu ga ita Amurkan . haka rahoton da Iraq Study Group da aka fi sani da hamilton / baker shima ya ja kunnen Amurka da ta riki Iran hanu bibbiyu in har tana son kafuwa a Iraki.

Akwai dalilai masu dunbin yawa dake tabbatar da shakikancin Amurka da Iran , kuma wannan su saba kamar yadda harshe da hakori ke sabawa , ko kamar yadda Amurka da Isra’ila ake kai ruwa rana wani lokacin , ko kuma Birtaniya .

Ko kadan banyi wannan rubutun don wanke wani dan siyasa ko wata kasa daga alaka da Amurka ko Isra’ila ba , koda kuwa ta zama kasar sunnah , don kuwa kowace kasa tana da alakokinta da wadannan kasashe biyu saidai wata tafi wata , innama nufina in gwadawa wadannan masu cika bakin cewa Kasar Iran ma’asumiya ce ga abokantaka da yahudu da Nasara , in sun sani amma suke boyewa suyi adalci su fadi gaskiya, in kuwa ana yaudaransu ne to ya kamata su ringa neman sani kan abu buwanda ke gudana .

Mudai agunmu masu neman dacewa da sunnar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi , ba’a umurcemu da bin Sa’udiya ba , don haka in tayi wani katobara , baya cikin adalci ace sai mun sama mata mafita ko mu wanketa da karya da gaskiya , Don haka abunda zai daddale gaskiya tsakanin shi’a da sunnah ba abunda sarki Abdullahi ko Husni Mubarak ko kuma a daya bangaren Ahmadi Najad ko Hasan Nasrallah suka yiba , innama abunyi shine a tambatayi ko wani dan shi’a meye matsayin Sahabban Manzo tsira da amincin Allah su tabbata masa agunka , ko A’isha uwar muminai , shin meye matsayin makashin sayyidina Umar mai raba karya da gaskiya, shin abun aje Hubbarensa ne ana neman tabarruki ? . shin Abuhuraira wanda ya kiyaye hadisan manzon Allah tsira da aminci ya tabbata masa makaryaci ne kwadayaiye ? , shin da gaske wai cewa a akidarku in Sha-sauraronku yazo sai ya tashi Saiyidai Abubakar da Umar ya azabtar dasu ?.

Sannan a waiwayi Ahlussunnah a tambayesu shin Akidar ta tanadi wata darajawa da kimatawa ga Sayyidina Aliyu wanda manzon Allah ya shaida cewa yana son Allah , kuma Allah yana sonsa ? , ko Hasan da Husaine wadanda manzon Allah yace sune shugannin samarukan aljanna ? .

Naku Alkalami.

4 comments:

Anonymous said...

Assalamu alaykum
ba shakka wannan bayani da malam auwal yagabatar bayani ne wanda duk wanda yake bibiyan rubuce-rubucen yan shia yasan cewa babu kage ko kari akai wannan shine hakikan wannan addini na yan shia wanda suke fake wa da addinin mu na islama suna dasa irn muna nan akidun su.saboda haka wannan yaza ma kalu bale ga malaman islama da su tashi tsaye wajen karantar da a al=umma hakikanin wannan addini na musulunci.kuma Allah yaka yawai ta islama samari masu kishin shi kamar su MALAM AUWAL.by yusuf raka

mohammed said...

assalamu alaikum,naji dadin yanda ka kare wannan rubutu naka,amma da kakara wannan tambayoyi wa yan sunnah;shin Annabi yayi nuni da abin da za a rike bayansa?meye taarifin sahabi a alkurani da kuma a hadisi?

Muhammad said...

Maxhabar Shi'anci ta iran abin kyamane ya Allah ka kiyayemu daga xamiyar shiga shi'a.

Anonymous said...

Hello there! I could have sworn I've visited this web site before but after looking at many of the posts I realized it's new to me.

Nonetheless, I'm certainly delighted I discovered it and I'll be book-marking it and checking
back frequently!

My page - landhausmode paul klauser kollbrunn